Leadership News Hausa:
2025-11-16@23:03:24 GMT

Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Published: 9th, March 2025 GMT

Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Liberpool na shirin lashe Premier League na bana kuma na 20 jimilla, za ta yi kan-kan-kan da yawan wanda Manchester United ta dauka a tarihi kuma Liberpool ce ta daya a kan teburin Premier na kakar nan da maki 67, sai Arsenal ta biyu mai maki 54.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Firimiya

এছাড়াও পড়ুন:

Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi

Sheikh Ahmad Gumi ya yi martani kan kiraye-kirayen da ake yi na kama shi, inda ya ce masu yin kiran na yi ne domin kawar da rawar da yake takawa wajen magance matsalar ’yan bindiga a Arewa.

Gumi, ya ce duk ganawar da yake yi da ’yan bindiga yana yi ne domin samar da zaman lafiya, kuma hukumomin tsaro sun san da komai.

Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio

Maganar ta sake fitowa fili ne bayan da ya sake jaddada cewa tattaunawa hanya ce da za ta iya kawo ƙarshen tashin hankali a karkara.

A cikin dogon saƙon da ya wallafa a Facebook a ranar Lahadi, Gumi ya soki masu cewa ya kamata a kama shi saboda ya ganawar da ya yi da shugabannin ’yan bindiga.

Ya bayyana kiran a matsayin don rai la’akari da irin ƙoƙarin da ya yi a baya domin daƙile matsalar tsaro a Arewa.

Ya ce ba shi niyyar goyon bayan masu laifi; kawai yana ƙoƙari rage tashin hankali da kuma shawo kan ’yan bindiga su miƙa wuya.

Gumi, ya ce ya yi muhimmin zama da mahara a Janairun 2021 a dajin Sabon Garin Yadi da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Kuma ya ce tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna ya je a lokacin d aka yi ganawar, wanda ya wakilci Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa.

Ya ce taron ya samu halartar ’yan bindiga da shugabanninsu sama da 600, kuma sun yi alƙawarin daina kai hare-hare idan gwamnati ta samar musu da wasu muhimman abubuwa.

“Na je dajin Sabon Garin Yadi tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna.”

“Wannan zama ɓangare ne na aikin samar da zaman lafiya, inda muka yi wa ’yan bindiga sama da 600 da shugabanninsu wa’azi, suka kuma amince za su ajiye makamai idan gwamnati ta samar musu da tsaro da ingantaccen rayuwa,” in ji shi.

Gumi, ya ce duk abin da ya yi bisa ƙa’ida ya yi sa, kuma hukumomi sun san da komai.

Ya ce maimakon mutane su kai su soke shi, kamata ya yi su tambayi dalilin da ya sa gwamnati ba ta yi buƙatun ’yan bindiga ba.

Sheikh Gumi ya kuma tambayi dalilin da ya sa wasu ke son a kama shi, alhali manufarsa ita ce kawo ƙarshen tashin hankali a Najeriya.

“To me zai sa kama ni? Domin na yi kira su ajiye makamai… ko saboda na faɗakar da al’umma game da labarin ’yan bindiga?”.

Gumi ya zargi masu sukarsa da nuna wariya, inda ya tunatar da su cewa kundin tsarin mulki ya bai wa kowa damar faɗin albarkacin bakinsa.

“Shin faɗin ra’ayi ba haƙƙinmu ba ne na kundin tsarin mulki ba? Shin kira da suke yi na a kama ni ba nuna son rai ba ne kuma zai iya haifar da tashin hankali?”.

Ya bayyana cewa buƙatun ’yan bindigar suka nema waɗanda suka haɗa da ababen more rayuwa, kariya daga kame ba bisa ƙa’ida ba, da hanankai musu hari ba idan sun miƙa wuya.

Ya ce babu ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan da aka aiwatar, wanda hakan ya wargatsa tattaunawar.

Gumi, ya ce kamata ya yi mutane su mayar da hankali kan mafita a aikace, ba zagi da fushi ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
  • NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji
  • Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi
  • Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda, sun kama mutum 94
  • Shugaban Iran Da Prime Ministan Iraqi Sun Tattaunawa Kan Batun Zabe Da Kuma Alakar Dake Tsakaninsu.
  • GORON JUMA’A
  • Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani