Aminiya:
2025-07-12@17:05:30 GMT

Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato

Published: 21st, June 2025 GMT

An yi wa wasu matafiya ɗaurin aure 12 kisan gilla bayan wasu mutane sun kai musu hari a yankin Mangu ta Jihar Filato sun kai musu hari.

Rahotanni sun bayyana cewa mutum 11 daga cikin matafiya suna samun kulawa a asibiti, bayan raunukan da suka samu a harin da aka kai musu a yankin Ƙaramar Hukumar Mangu a ranar Juma’a.

Aminiya ta samu labarin cewar an kai wa matafiya hari ne da misalin ƙarfe 8 na dare, a lokacin da su mutum 31, ciki har da mata da ƙananan yara, a cikin wata bas mallakin Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta Zariya.

Ayarin ’yan daurin auren da aka kai wa harin sun fito ne daga yankin Basawa da ke Zariya a Jihar Kaduna, lokacin da maharan suka tare su a kusa da yankin Ƙaramar Hukumar Qu’an Pan, suka kashe  mutum 12, ciki har da direban motar, wanda ma’aikacin jami’ar ne.

Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila

Babban Limamin Masallacin Juma’a na Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), da ke Mangu, Sheikh Suleiman Haruna, ya tabbatar da faruwar lamarin, da cewa an ajiye gawarwakin a Babban Asibitin Mangu.

Sheikh Suleiman Haruna, ya ce, “Matafiya 31 ne a motar. Mun samu gawarwakin mutum takwas, amma mun roƙi jami’an tsaro su taimaka wajen kawo ragowar gawarwaki huɗu da suka rage.

“Muna tare da Shugaban Ƙaramar Hukumar Mangu kuma yana iya bakin ƙoƙarinsa a kan lamarin.”

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin, Ibrahim Umar, ya ce, “Mun kusa kaiwa Qu’an Pan bikin ɗaurin auren ɗan uwanmu, amma muka yi ɓatan kai saboda ba mu san hanyar ba.

“Mun tsaya tambayar wasu mutane kwatance, kafin mu farga har sun yi mana ƙawanya sun zagaye motar ta kowace kusurwa, suna ihu cewa a kashe mu, mu Hausawa ne.

“Daga nan suka fara duka suna kawo mana hari da muggan makamai. Direban suka fara kashewa kafin sauranmu, suka ƙona motar da gawarwakin mutane a ciki. Yanzu muna asibiti ana jinyar mu.”

Wakilimmu ya tuntuɓi kakakin ’yan sanda na Jihar Filato, DSP Alfred Altau, kuma jami’in ya shaida masa cewa yana sane da lamarin, amma sai nan gaba zai fitar da sanarwa a hukumance bayan tantance haƙiƙanin abin da ya faru.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure mahara Matafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi

Sojojin Operation SAFE HAVEN da ke aiki a Arewacin Najeriya, sun kama wani mutum da ake zargi da garkuwa da mutane a kan hanyar Wamba zuwa Jos, tare da kuɗi Naira miliyan 13 da kuma makamai

Wannan kamen ya faru ne a ranar Laraba, 9 ga watan Yuli 2025, a wani shingen bincike da sojoji suka kafa a Agameti, a Ƙaramar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna.

Muna tunanin sayar da matatun man Najeriya — NNPCL Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda

A cewar mai magana da yawun rundunar, Manjo Samson Zhakom, sojojin sun dakatar da wata mota ƙirar Volkswagen mai lamba JJN 336 YZ, ɗauke da mutane uku.

Amma biyu daga cikin su sun tsere kafin a fara bincike.

Bayan duba motar, sojojin sun gano bindigogi biyu ƙirar AK-47, harsashi da yawa, da kuma jini a cikin motar.

Wanda aka kama ya yi ƙoƙarin bai wa sojoji cin hancin kuɗi domin su sake shi, amma suka ƙi amincewa.

Sojojin na ci gaba da ƙoƙarin kamo waɗanda suka tsere domin tabbatar da doka da oda a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Direba ya tsere da buhun masara 463
  • Sojoji sun kama mai garkuwa da mutane da bindigogi
  • An tsare mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Kotu ta aike mutum 20 da ake zargi da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa
  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Neja