Aminiya:
2025-09-20@06:40:35 GMT

Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato

Published: 21st, June 2025 GMT

An yi wa wasu matafiya ɗaurin aure 12 kisan gilla bayan wasu mutane sun kai musu hari a yankin Mangu ta Jihar Filato sun kai musu hari.

Rahotanni sun bayyana cewa mutum 11 daga cikin matafiya suna samun kulawa a asibiti, bayan raunukan da suka samu a harin da aka kai musu a yankin Ƙaramar Hukumar Mangu a ranar Juma’a.

Aminiya ta samu labarin cewar an kai wa matafiya hari ne da misalin ƙarfe 8 na dare, a lokacin da su mutum 31, ciki har da mata da ƙananan yara, a cikin wata bas mallakin Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta Zariya.

Ayarin ’yan daurin auren da aka kai wa harin sun fito ne daga yankin Basawa da ke Zariya a Jihar Kaduna, lokacin da maharan suka tare su a kusa da yankin Ƙaramar Hukumar Qu’an Pan, suka kashe  mutum 12, ciki har da direban motar, wanda ma’aikacin jami’ar ne.

Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila

Babban Limamin Masallacin Juma’a na Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), da ke Mangu, Sheikh Suleiman Haruna, ya tabbatar da faruwar lamarin, da cewa an ajiye gawarwakin a Babban Asibitin Mangu.

Sheikh Suleiman Haruna, ya ce, “Matafiya 31 ne a motar. Mun samu gawarwakin mutum takwas, amma mun roƙi jami’an tsaro su taimaka wajen kawo ragowar gawarwaki huɗu da suka rage.

“Muna tare da Shugaban Ƙaramar Hukumar Mangu kuma yana iya bakin ƙoƙarinsa a kan lamarin.”

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin, Ibrahim Umar, ya ce, “Mun kusa kaiwa Qu’an Pan bikin ɗaurin auren ɗan uwanmu, amma muka yi ɓatan kai saboda ba mu san hanyar ba.

“Mun tsaya tambayar wasu mutane kwatance, kafin mu farga har sun yi mana ƙawanya sun zagaye motar ta kowace kusurwa, suna ihu cewa a kashe mu, mu Hausawa ne.

“Daga nan suka fara duka suna kawo mana hari da muggan makamai. Direban suka fara kashewa kafin sauranmu, suka ƙona motar da gawarwakin mutane a ciki. Yanzu muna asibiti ana jinyar mu.”

Wakilimmu ya tuntuɓi kakakin ’yan sanda na Jihar Filato, DSP Alfred Altau, kuma jami’in ya shaida masa cewa yana sane da lamarin, amma sai nan gaba zai fitar da sanarwa a hukumance bayan tantance haƙiƙanin abin da ya faru.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure mahara Matafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista

Sabuwar mutum-mutumi ta fasahar AI da aka kirkira kuma aka nada mukamin minista a ƙasar Albania ta yi jawabi a karon farko a gaban majalisar dokokin kasar.

A ranar Alhamis ce dai ministan ya bayyana gaban majalisar, inda ya kare rawar da zai taka a gwamnati, yana mai cewa, “Ban zo don na maye gurbin mutane ba, sai dai don taimaka musu.”

Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi

Wannan minista ta AI wacce aka sanya masa suna Diella, ma’ana “rana” a harshen Albania, ita ce ministar gwamnati ta farko a duniya da aka ƙirƙira ta hanyar fasahar AI.

Firaministan Albania, Edi Rama, ne ya naɗa shi a makon da ya gabata.

A cikin wani faifan bidiyo da aka nuna a majalisa, Diella ta bayyana a matsayin mace sanye da kayan gargajiya na Albania, inda ta ce: “Wasu sun ce ba na kan dokar kundin tsarin mulki saboda ni ba mutum ba ce.”

Diella ta ƙara da cewa: “Bari in tunatar da ku, babban hatsarin da ke tattare da kundin tsarin mulki ba na injuna ba ne, na masu mulki ne.”

A makon da ya gabata, Firaminista Rama ya bayyana cewa Diella za ta kula da dukkan al’amuran kwangiloli na gwamnati, domin tabbatar da cewa an kawar da cin hanci gaba ɗaya, kuma duk kuɗaɗen gwamnati da aka sanya a cikin tsarin kwangila za su kasance a bayyane.

An ƙaddamar da Diella a watan Janairu a matsayin mataimakiyar fasahar AI da ke taimaka wa jama’a wajen amfani da dandalin e-Albania, wanda ke bayar da takardu da ayyuka na gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An cafke mutum 6 kan tono gawa a kabari don yin asiri a Gombe
  • Mutum 1,666 ne suka kashe kansu a Legas cikin shekaru biyar – ’Yan sanda
  • Akasarin masu kai mana hare-hare daga jihohin da suka kewaye mu suke – Gwamnatin Filato
  • Cutar Kwalara ta kashe mutum 58 a Bauchi
  • ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
  • Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista
  • An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja