Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Published: 24th, June 2025 GMT
Haka kuma wasu ƙungiyoyi a Turai sun nuna sha’awar ɗaukar ɗan wasan.
Majiyoyi sun bayyana cewa Brentford na son a ce darajar Mbeumo ta kai irin kuɗin da United ta biya wajen ɗauko Cunha kafin su yarda su sayar da shi.
Mbeumo ya zura ƙwallaye 20 a kakar wasan da ta gabata, kuma ya taimaka aka zura wasu tara.
Sai dai akwai yiwuwar shi da abokin wasansa na tawagar Kamaru, Andre Onana, ba za su buga wasannin farko na sabuwar kakar wasa ba saboda za su wakilci Kamaru a gasar cin kofin ƙasashen Afirka da za a buga a Maroko.
Kamaru za ta fara buga wasa da Gabon ranar 24 ga watan Disamban 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa
Wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Alƙalin Babbar Kotun Jihar Bayelsa, Ebiyerin Omukoro.
Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Asabar a unguwar Ekeki, kusa da babban titin Melford Okilo a Yenagoa, babban birnin jihar.
Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a FilatoRahotanni sun bayyana cewa, mutanen sun isa a cikin mota ƙirar Hilux, sanye da baƙaƙen kaya.
Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, maharsn sun kutsa kai gidan cin abincin da alƙalin ke ciki kuma suka tilasta masa shiga motarsu.
Har zuwa yanzu, ba a san inda suka kai shi ba, kuma babu wani saƙo ko buƙatar kuɗin fansa daga masu garkuwar.
Hakazalika ba a san dalilin da ya sa suka sace shi ba.
Wannan ba shi ne karon farko da aka sace mutum a yankin ba, domin an je har gida an sace wani ɗan jarida mai suna Oyins Egrenbido.
Wasu hotuna da bidiyo da suka karaɗe shafukan sada zumunta sun nuna yadda aka kama alƙalin tare da jefa shi cikin motar ƙirar Hilux.
Har yanzu Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bayelsa, ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da sace alƙalin.