Leadership News Hausa:
2025-09-24@15:47:02 GMT

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Published: 22nd, June 2025 GMT

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Ɗan wasan gaban Manchester United Marcus Rashford ya ce zai so ya taka leda tare da matashin ɗan wasa Lamine Yamal a Barcelona, Rashford mai shekaru 27, wanda ya shafe rabin kakar wasan bara ya na zaman aro a Aston Villa, a halin yanzu yana atisayen ƙara kuzari a ƙasar Sifaniya kafin a fara wasannin share fage na kulob ɗin, yayin da ake ta raɗe raɗin makomarsa a United.

Lokacin da aka tambaye shi game da yiwuwar yin wasa tare da Yamal, Rashford ya ce: “E, tabbas, kowa yana so ya yi wasa tare da mafi kyawun dan wasa, don haka nima inada wannan burin kuma zamu gani, Yamal, mai shekaru 17, ya taka rawar gani sosai yayin da Barcelona ta lashe kofuna uku a bana, kuma ta kai wasan kusa da na karshe a gasar zakarun Turai, hakazalika ya kuma taka rawar gani a nasarar da kasar Sifen ta samu a Euro 2024.

Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or? Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

Rashford ya ƙara da cewa “Ba kowa ne zai iya yin abinda Yamal yayi a cikin shekaru 16-17 ba, don haka lallai akwai wata baiwa dangane da matashin ɗan wasan, Yana da matuƙar fikira idan ka kalli yadda yake sarrafa kwallo a kafarshi” Inji Rashford, rahotanni a watan Afrilu sun nuna cewa Rashford yana jin cewa da wuya ya sake bugawa Manchester United wasa a karkashin Ruben Amorim.

A watan Disamba ne dan ƙasar Portugal ɗin ya fitar da shi daga cikin tawagar United, kafin ya shafe sauran kakar a Aston Villa a matsayin aro, Daraktan wasanni na Barcelona Deco a baya ya ce kulob din yana son Rashford da Luis Diaz na Liverpool, sai dai duk da sha’awar da kulob din na Catalan ya nuna, kudi na iya zama cikas idan suka yi yunkurin siyan Rashford.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barcelona Rashford Yamal a Barcelona Rashford ya

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance

Faransa ta bi sahun Birtaniya, Australia da Canada da sauran ƙasashen duniya sama da 140 da suka amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ’yanci.

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ne ya tabbatar da amincewar gwamnatinsa na kafa ƙasar Falasdinu a hukumance.

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS NEF za ta ƙaddamar da taron zuba jari don bunƙasa Arewa

Macron ya bayar da tabbacin ne a yayin da yake jawabi a babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York.

Mista Macron ya ce lokaci ya yi da ya kamata a kawo ƙarshen yaƙin Gaza tare da sakin sauran Isra’ilawa 48 da Hamas ke garkuwa da su.

Ya ce lokaci kaɗan ne ya rage wa duniya ta iya wanzar da zaman lafiya, don haka ya ce bai kamata a jira ba.

Mista Macron ya yi Allah-wadai da harin na ranar 7 ga watan Oktoba da Hamas ta kai wa Isra’ila.

Shugaban na Faransa ya ce yana son ganin an samar da zaman lafiya a yankin ta hanyar samar da ƙasashe biyu masu cin gashin kai da ke zama makwabtan juna.

“Babu wata hujja na ci gaba da yaƙin Gaza”, in ji Macron, yana mai ƙarawa da cewa “ya kamata a kawo ƙarshen komai.”

A yau ne dai tawagar jami’an diflomasiyyan Falasɗinu ta gudanar da bikin ɗaga tutar ƙasar a birnin Landan, kwana guda bayan da Birtaniya ta amince da Falasɗinu a matsayin kasa mai cin gashin kanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu, sun sace mutum 8 a Kwara
  • Yada labaran karya a intanet babban laifi ne a Musulunci – Sheikh Ibrahim Khalil
  • An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
  • Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh ya rasu yana da shekara 82
  • Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
  • Faransa ta amince da ’yancin ƙasar Falasɗinu a hukumance
  • Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025?
  • Ballon d’Or: ’Yan wasa 5 da ke iya lashe kyautar 2025 
  • Kwamandan Sojan Iran: Ba Za Mu Taba Wasa Da Manufofinmu Na Kasa Ba
  • Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka