Da yake gabatar da kudirin, dan majalisar, Abdullahi ya nuna matukar damuwarsa kan kisan da aka yi wa matafiyan a ranar Juma’a, a lokacin da suka bata kan hanyarsu a yayin da suke tafiya don halartar wani daurin aure a karamar hukumar Mangu.

 

Ya ce, wadanda aka kashen, ba su dauke da wani makami, kawai suna kan hanyarsu ne ta zuwa daurin aure, wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari tare da kashe su, lamarin da ya jefa ‘yan uwan matafiyan cikin jimami.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokokin Yawon Buɗe Ido da Zartar da Shari’a

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokoki guda biyu masu muhimmanci da nufin ƙarfafa harkar yawon buɗe ido da hanzarta gudanar da shari’a a faɗin jihar.

Shugaban majalisar, Yusuf Dahiru Liman, ne ya sanar da amincewar majalisar  yayin zaman, ta wanda aka gudanar a harabar majalisar da ke Kaduna.

 

Dokar farko mai taken “Dokar Kafa Hukumar Kula da Yawon Buɗe Ido, Gidajen Tarihi, Shata Wurare, Lambuna da Wuraren Hutu na Jihar Kaduna, 2024”, na da nufin bunƙasa harkar yawon buɗe ido da raya al’adu a  jihar.

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Yusuf Dahiru Liman

Da yake gabatar da rahoton kwamitin, Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Harkokin Fasaha, Shari’a da Ilimi, Magaji Suleiman, ya bayyana cewa kwamitin ya gudanar da cikakken bincike kan kudirin kuma ya fahimci cewa yana da amfani wajen haɓaka yawon buɗe ido da al’adu.

Magaji Suleiman ya ce idan aka fara aiki da hukumar, za ta inganta shata wurare, lambuna da wuraren shakatawa a jihar, wanda hakan zai ja hankalin masu zuba jari daga cikin gida da waje.

A nasa jawabin, wanda ya dauki nauyin gabatar da kudirin, Mr. Henry Marah, ya bayyana cewa hukumar za ta taka rawa wajen farfaɗo da al’adun gargajiya na jihar Kaduna wacce ke da yawan kabilu daban daban.

Ya ƙara da cewa dokar za ta taimaka wajen samar da kuɗaɗen shiga ga jihar, ƙirƙiro guraben ayyukan yi ga matasa da kuma cusa tarbiyar al’adu ga matasa masu tasowa.

Barista Emmanuel Kantiyok

Har ila yau, Majalisar ta kuma amince da gyara dokar gudanar da shari’ar laifuka ta Jihar Kaduna ta shekarar 2017.

Da yake gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin Shari’a na Majalisar, Barista Emmanuel Kantiyok, ya bayyana cewa gyaran dokar zai taimaka wajen gudanar da shari’a a kan lokaci da kuma tabbatar da adalci ba tare da la’akari da matsayin mutum ba.

Barista Kantiyok ya ce gyaran dokar zai taimaka wajen rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma ƙara wa talakawa kwarin gwiwa ga tsarin shari’a.

Majalisar ta amince da dokokin ne ta hanyar ƙuri’ar murya da ‘yan majalisar suka kada, karkashin jagorancin Shugaban Majalisar, Yusuf Dahiru Liman.

Daga ƙarshe, majalisar ta tafi hutu kuma za ta dawo zaman ta a ranar 9 ga Satumba, 2025.

 

Shamsuddeen Mannir Atiku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasashen Larabawa Da Kungiyoyinsu Sun Yiu Allah Wadai Da Shirin ‘Yan Shayoniyya Kan Gaza
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokokin Yawon Buɗe Ido da Zartar da Shari’a
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara
  • An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara
  • ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
  • An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna
  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi