Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
Published: 23rd, June 2025 GMT
Tun da ka yi karatu a Italiya, yaya kake kwatanta ci gaban Kano, da na wasu biranen zamani da ka sani?
Wannan tambaya ce mai amfani. Birane irin su Milan da Florence da Turin, suna da dogon tarihi a fannin ci gaban birane amma abin da ke bambanta Kano a yanzu shi ne saurin aiki da kuma hangen nesa, kuma wannan gwamnati tana da tsari a fagen.
Wasu suna cewa shekaru biyu ba su isa a auna nasarar gwamnati ba. Mene ne ra’ayinka gane da hakan?
A wannan magana, ban yarda da ita ba. Shekaru biyu ƙarƙashin Injiniya Abba Kabir Yusuf, sun haifar da abubuwan da wasu shugabanni ba su iya yi ba a cikin shekaru takwas da suka yi suna mulki ba. Duk abinda aka gina kan tubali nagari, ba sai an jira dogon lokaci ba za a fara ganin tasirinsa, abin da kawai ake buƙata shi ne jagoranci nagari. Kuma hakan muna da shi a yanzu. Ayyukan da ya yi cikin shekaru biyu ya cancanci a rubuta su cikin tarihi.
Wasu na cewa irin waɗannan shugabanni su na da buƙatar a ba su dama su ci gaba da mulki fiye da iyakar wa’adin da kundin tsarin mulki ya tanada. Me za ka ce akan haka?
Wannan gaɓa ce mai mahimmanci, wanda lokaci ya yi da ya kamata mu sauya yadda muke kallon shugabanci. Idan muna da shugaba mai hangen nesa da bayar da sakamako, kuma wanda ke tafiyar da mulki kan buƙatun al’umma kamar Injiniya Abba Kabir Yusuf, me zai hana a ɗora da ci gaban da yake kawo wa? Da alama kamar muna hukunta nasara ne idan muka taƙaita irin wannan shugaba zuwa wa’adi biyu wato “4+4”. Irin waɗannan shugabanni misali ne ba kawai ga Nijeriya ba, har ma ga nahiyar Afirka da duniya baki ɗaya. Idan akwai buƙatar sauya tsarin mulki don bayar da damar ci gaba da irin wannan jagoranci, to ya dace mu fara tattaunawa a kan haka, don ci gaba bai kamata a katse shi ba saboda al’ada.
A ƙarshe wane saƙo za ka bai wa jama’ar Kano da matasa ‘yan kasuwa irinka?
Ga jama’ar Kano, wannan lokacinmu ne da za mu tallafa wa wannan jagoranci mai hangen nesa ta hanyar bayar da gudummawa wajen ɗaukar nauyin ci gaban da ke faruwa a garuruwan mu. Ga matasa ‘yan kasuwa kuma ku duba Kano yanzu. Dama tana bayyana a ɓangarori daban-daban daga gine-gine, da fasahar zamani (IT), da masana’antu, har ma da yawon buɗe ido. Lokaci ne da ya dace mu fara tunani mai zurfi, tare da shirin ƙara jajircewa don bayar da gudummawa wajen gina sabuwar Kano.
Gwamna na cika shekaru biyu a mulki, mene ne saƙonka na ƙarshe?
A ƙarshe, ina mika gaisuwa ta musamman ga mai girma gwamna, Injiniya Abba Kabir Yusuf, bisa cikarsa shekaru biyu kan karagar shugabanci nagari. Haƙiƙa ya nuna mana yadda salon jagoranci nagari ya ke, tare da yadda ake fifita muradun jama’a a tsarin shugabanci, muna miƙa saƙon gaisuwa tare da nuna alfahari da shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Arch Ali Hassan Tsara Birane shekaru biyu
এছাড়াও পড়ুন:
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
Ya ƙara da cewax gwamnatinsa ta fara gyara daga tushe, inda ilimi ya zama ginshiƙin farko. “Shekaru takwas kafin mu hau mulki, ɗalibanmu ba su samun takardun WAEC, sannan tsawon shekaru biyu suna fama da matsalar NECO. Na biya Naira Biliyan huɗu don magance wannan matsala,” inji shi.
Gwamnan ya bayyana irin matsalolin da ya gada, yana mai cewa: “Na samu asusun gwamnati da naira miliyan huɗu kacal. Ma’aikata suna karɓar albashi cikin rashin tabbas, babu ruwa, asibitoci kuwa suna cikin mummunan yanayi.”
Lawal ya ce, ya sake fasalin tsarin gwamnati, inda ya rage yawan kwamishinoni da manyan sakatarorin don rage ɓarna da ƙara inganci. “Yanzu muna daga cikin jihohi mafi ci gaba wajen tara haraji, inda kuɗaɗen shiga suka ƙaru da fiye da kaso 300 cikin 100,” inji shi.
Ya bayyana cewa gwamnatin sa ta gina ko ta gyara makarantu sama da 500, tare da aiwatar da ayyukan da kuɗinsu ya kai biliyan N10 a kowace ƙaramar hukuma. Duk da cewa ana cire biliyan 1.2 a kowane wata daga kuɗaɗen gwamnati don biyan basussuka, an biya bashin fansho da giratuti na fiye da biliyan N13.6 da aka tara tun shekarar 2011.
A ɓangaren tsaro, Lawal ya ce jihar ta ɗan sami sauƙi bayan kafa rundunar tsaron gida, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin tabbatar da amfanin mulki ya kai ga talaka.
A nasa jawabin, Babban Editan LEADERSHIP, Azu Ishiekwene, ya ce an bai wa gwamnan wannan lambar yabo ne saboda irin nasarorin da ya samu a fannonin tsaro, ilimi, lafiya da gine-gine, yana mai cewa “jarida tana da alhakin duba gwamnati, amma kuma tana da haƙƙin yabawa idan ana yin daidai.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA