Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
Published: 23rd, June 2025 GMT
Tun da ka yi karatu a Italiya, yaya kake kwatanta ci gaban Kano, da na wasu biranen zamani da ka sani?
Wannan tambaya ce mai amfani. Birane irin su Milan da Florence da Turin, suna da dogon tarihi a fannin ci gaban birane amma abin da ke bambanta Kano a yanzu shi ne saurin aiki da kuma hangen nesa, kuma wannan gwamnati tana da tsari a fagen.
Wasu suna cewa shekaru biyu ba su isa a auna nasarar gwamnati ba. Mene ne ra’ayinka gane da hakan?
A wannan magana, ban yarda da ita ba. Shekaru biyu ƙarƙashin Injiniya Abba Kabir Yusuf, sun haifar da abubuwan da wasu shugabanni ba su iya yi ba a cikin shekaru takwas da suka yi suna mulki ba. Duk abinda aka gina kan tubali nagari, ba sai an jira dogon lokaci ba za a fara ganin tasirinsa, abin da kawai ake buƙata shi ne jagoranci nagari. Kuma hakan muna da shi a yanzu. Ayyukan da ya yi cikin shekaru biyu ya cancanci a rubuta su cikin tarihi.
Wasu na cewa irin waɗannan shugabanni su na da buƙatar a ba su dama su ci gaba da mulki fiye da iyakar wa’adin da kundin tsarin mulki ya tanada. Me za ka ce akan haka?
Wannan gaɓa ce mai mahimmanci, wanda lokaci ya yi da ya kamata mu sauya yadda muke kallon shugabanci. Idan muna da shugaba mai hangen nesa da bayar da sakamako, kuma wanda ke tafiyar da mulki kan buƙatun al’umma kamar Injiniya Abba Kabir Yusuf, me zai hana a ɗora da ci gaban da yake kawo wa? Da alama kamar muna hukunta nasara ne idan muka taƙaita irin wannan shugaba zuwa wa’adi biyu wato “4+4”. Irin waɗannan shugabanni misali ne ba kawai ga Nijeriya ba, har ma ga nahiyar Afirka da duniya baki ɗaya. Idan akwai buƙatar sauya tsarin mulki don bayar da damar ci gaba da irin wannan jagoranci, to ya dace mu fara tattaunawa a kan haka, don ci gaba bai kamata a katse shi ba saboda al’ada.
A ƙarshe wane saƙo za ka bai wa jama’ar Kano da matasa ‘yan kasuwa irinka?
Ga jama’ar Kano, wannan lokacinmu ne da za mu tallafa wa wannan jagoranci mai hangen nesa ta hanyar bayar da gudummawa wajen ɗaukar nauyin ci gaban da ke faruwa a garuruwan mu. Ga matasa ‘yan kasuwa kuma ku duba Kano yanzu. Dama tana bayyana a ɓangarori daban-daban daga gine-gine, da fasahar zamani (IT), da masana’antu, har ma da yawon buɗe ido. Lokaci ne da ya dace mu fara tunani mai zurfi, tare da shirin ƙara jajircewa don bayar da gudummawa wajen gina sabuwar Kano.
Gwamna na cika shekaru biyu a mulki, mene ne saƙonka na ƙarshe?
A ƙarshe, ina mika gaisuwa ta musamman ga mai girma gwamna, Injiniya Abba Kabir Yusuf, bisa cikarsa shekaru biyu kan karagar shugabanci nagari. Haƙiƙa ya nuna mana yadda salon jagoranci nagari ya ke, tare da yadda ake fifita muradun jama’a a tsarin shugabanci, muna miƙa saƙon gaisuwa tare da nuna alfahari da shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Arch Ali Hassan Tsara Birane shekaru biyu
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna baƙin cikinsa kan kisan wasu matafiya daga Jihar Kaduna da aka yi a Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.
Matafiyan sun fito ne daga Zariya suna kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure, yayin da wasu ɓata-gari suka farmake su.
HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba SaniGwamnan ya ce wannan kisa abin takaici ne kuma rashin imani ne da ya saɓa wa doka.
Ya buƙaci a yi adalci cikin gaggawa.
Haka kuma ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kaduna, iyalan mamatan, da sauran waɗanda abin ya shafa.
A cewar sanarwar da Daraktan Yaɗa Labaran Gwamnatin Jihar Gombe, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar, Gwamna Yahaya ya yaba wa gwamnati da ‘yan sanda a Jihar Filato bisa kamo wasu da ake zargi da hannu a kisan.
Gwamnan ya buƙaci a yi bincike na gaskiya, a gurfanar da waɗanda ke da hannu domin a hukunta su, sannan a hana irin hakan faruwa a gaba.
Haka kuma, ya roƙi al’ummar Filato da Kaduna da sauran maƙwabta da su zauna lafiya, su guji ɗaukar fansa.
Ya ce Gwamnonin Arewa za su ci gaba da haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.
“Ina tabbatar muku cewa kare rayuka da dukiyoyin al’umma shi ne babban burinmu. Za mu yi aiki tare har sai an kawo ƙarshen wannan matsala,” in ji Gwamnan.