“Ina so in yi kira ga NNPYA da duk sauran kungiyoyi da daidaikun mutane da ke cikin wannan ikirari da su daina wannan kiran, a maimakon haka, su mayar da karfinsu wajen marawa Shugaba Tinubu baya a yunkurinsa na magance dimbin kalubalen da kasarmu ke fuskanta.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Barazanar Trump: Ya kamata shugabannin Najeriya su farka daga bacci — Bishop Kukah

Bishop Matthew Kukah, na Cocin Katolika da ke Jihar Sakkwato, ya ce barazanar da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na kawo wa Najeriya ya farkar da shugabannin ƙasar nan. 

Trump, ya zargi Najeriya da cin zarafin Kiristoci tare da barazanar janye tallafin Amurka ko kuma ɗaukar matakin soja domin “ceto Kiristoci” a ƙasar.

Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu — Tinubu

Sai dai Shugaba Bola Tinubu, ya musanta wannan zargi, inda ya bayyana cewa Najeriya kasa ce mai cikakkiyar dimokuraɗiyya mai mutunta ’yancin yin addini.

Da yake jawabi a wajen bikin cika shekaru 60 na ɗan jarida Reuben Abati a Jihar Legas, Kukah, ya ce kalaman Trump na nuna akwai matsaloli a Najeriya.

“Muna ganin Trump a matsayin  matsala. Amma Trump alama ce ta rashin lafiyar da ke cikin ƙasarmu,” in ji Kukah.

“Ko Trump ne ko wani daban ya tunzuramu, lokaci ya yi da Najeriya za ta farka.”

Ya kuma soki rashin wuraren yawon buɗe ido da abubuwan tarihi da za su nuna ainihin abubuwan da Najeriya ta mallaka.

“Idan wani ya zo Najeriya yau, ina za ka kai shi? Dole mu sake gina ƙasarmu da kuma bayyana tarinhinmu a matsayin ’yan ƙasa,” in ji shi.

Kukah ya yi kira ga ’yan Najeriya da su yi tunani mai zurfi tare da ɗaukar nauyin gina ƙasa mai haɗin kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Trump: Ya kamata shugabannin Najeriya su farka daga bacci — Bishop Kukah
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu