Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Published: 24th, June 2025 GMT
Eze ya gode wa waɗanda suka kafa ADA saboda ƙoƙarinsu na ceton Nijeriya daga hannun shugabannin da ba sa bin tsarin dimokuraɗiyya.
Ya ce sun nuna ƙwazo da ƙaunar ƙasa.
Ya ce, “Kun nuna bajinta da kishin ƙasa ta hanyar ƙoƙarin ƙwato mulki daga hannun shugabannin da suka haddasa rikice-rikice, garkuwa da mutane, talauci, yunwa da kunya ga ƙasar nan.
Eze ya kuma yi addu’ar cewa Allah Ya taimaka musu su samu nasarar ceto Nijeriya daga hannun shugabanni marasa ƙwarewa da tausayi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Siyasa takara Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su
Iyalan mafarauta 16 ’yan Jihar Kano da aka yi wa kisan gilla a garin Uromi da ke Jihar Edo sun yi zargin cewa gwamnati ta yi watsi da su.
Wasu daga cikin waɗanda suka tsallake rijiya da baya a harin da kuma iyalan waɗanda aka kashe, sun bayyana cewa alƙawarin kuɗin magani da tallafi da kuma diyya fa gwamnatocin jihohin Edo da Kano suka yi musu bai wuce fatar baki ba.
Ayarin farautan sun baro garin Fatakwal na Nijar Ribas ne, a hanyarsu ta komawa gida domin bikin Ƙaramar Sallah, amma wasu ’yan banga a Uromi suka tare su, suka yi musu kisan gilla.
Akasarin mafarautan sun fito ne daga yankin Toronkawa da ke Ƙaramar Hukumar Bunkure ta Jihar Kano, tare da abokansu daga ƙananan hukumomin Garko da Kibiya da Rano.
Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu’Yan kaɗan daga cikinsu ne suka sha da ƙyar a harin na Uromi na ranar 28 ga watan Maris, wanda ya sha tofin Allah-tsine daga ɓangarori daban-daban.
’Yan sanda sun bayyana cewa sun kama mutum 14 bisa zargin hannunsu a harin, a yayin da gwamnatocin jihohin Kano da kuma inda abin ya faru, suka yi alƙawarin ɗaukat matakan da suka dace na tallafi ga waɗanda abin ya shafa da iyalansu da kuma tabbatar da cewa an hukunta masu laifin.
A watan Afrilu Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, ya sanar da kafa kwamitin bincike na haɗin gwiwa da Gwamnatin Tarayya kan lamarin.
Gwamna Okpebholo ya sanar da haka ne bayan mataimakin Gwamnan Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jagoranci jami’an gwamnatin Kano suka yi takakkiya zuwa Edo bayan kisan da aka yi wa Kanawan.
Daga bisani Okpebholo ya kai ziyarar ta’aziyya Kano, inda ya yi alƙawarin biyan diyya ga iyalan mamatan da kuma majinyatan da harin ya shafa.
A nasa jawabin Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda ya jagoranci Okpebholo zuwa garin Toronkawa, ya jaddada cewa gwamnatin jihar za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin an biya cikakken diyya ga iyalan. Ya kuma yi musu alƙawarin tallafi na kuɗaɗe da kayan abinci.
Gwamnatocin Kano da Edo sun yi gumAminiya ta tuntuɓi Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Ibrahim Garba Waiya, wanda kuma mamba ne a kwamitin binciken, kan dalilin rashin cika alƙawuran da gwamnatin jihar ta yi wa mutanen da abin ya shafa, amma ya ƙi cewa komai.
Haka shi ma Kwamishinan Jihar Edo, Paul Ohonbamu da Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan jihar, Free Itua, ba su amsa kiranmu ba ko rubutattun tambayoyin da aka tura musu.
Wakilinmu ya tuntuɓi shugaban al’ummar Hausawa a Jihar Edo, Alhaji Badamasi Saleh, amma ya bayyana cewa ba shi da masaniya game da ko gwamnatin jihar ta biya diyyar da ta yi wa mutanen alƙawari.
Ba a cika mana alƙawari baA garin Toronkawa kuma, iyalai da ragowar mafarautan da harin ya shafa sun ce ba a cika alƙawarin ba.
Ɗaya daga cikin mafarautan da ya tsallake rijiya da baya, Ibrahim Isah, ya tabbatar da hakan, inda ya ƙara da cewa, “Yanzu da ƙyar nake iya kula da iyalina. Yarana ’yan ƙanana ne ballantana su tallafa min.
“An yi mana alƙawarin za a kula da mu a asibiti, amma daga aljihuna na kashe kuɗin jinya N40,000, duk da haka ban samu kulawar da ta dace ba.”
Ya ce duk da alƙawarin tallafin abinci da sauransu da Gwamnatin Kano ta yi musu, amma ba su gani a ƙasa. “Sun ce sun kawo mana kuɗi da abinci, amma dai ba mu komai ba.
“Mun je sakatariyar ƙaramar hukuma, aka ce ciyaman ya tafi Saudiyya, amma mataimakinsa ya ce suna aiki a kan lamarin,” a cewar Malaman Ibrahim ɗan shekara 45.
Malama Zahura Haruna, matan ɗaya daga cikin mafarautan da aka kashe, ta ce, “Rayuwa ta yi mana ƙunci, yanzu na zama nauyi ga surukaina, da ma shi ne mai ƙarfin gidan. Yanzu da maƙwabta muka dogara don samun abinci.”
A Ƙaramar Hukumar Kibiya kuma, Malam Bala Dutse, wanda aka kashe ɗansa Ahmadu a harin Ironsi, ya bayyana wa wakilinmu cewa ba su ji komai daga ɓangaren gwamnati ba, amma, “aƙalla ya kamata su fito su yi mana bayanin abin da suka tsara yi game da biyan diyyan.”
Wata mai takaba daga cikin matan mafarautan da aka kashe, Hauwa’u Isah, ta ce, “sun yi mana alƙawarin adalci, amma kullum sai ka ga abin kamar kalaman siyasa ne kawai.”
Amma Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Kibiya, Nasiru Adam Abdulaziz, ya jaddada aniyar ƙaramar hukumar ta mama wa waɗanda abin ya shafa adalci.
Ya ce, “Waɗannan iyalan sun cancanta a yi musu bayani kuma ina da ƙwarin gwiwa cewa gwamnati za ta yi abin da ya dace.”