Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha
Published: 24th, June 2025 GMT
Shugaban Mali, Assimi Goita da takwaransa na Rasha, Vladimir Putin, sun rattaba hannu kan yarjejeniyar makamashin nukiliya a fadar Kremlin da ke birnin Moscow.
Wannan dai na cikin wasu yarjejeniyoyi da Mali da Rasha suka rattaba hannu waɗanda aka tsaro domin inganta alaƙar kasuwanci da tattalin arziki.
Shugaba Vladimir Putin ya shaida wa shugaban kasar ta Afirka ta Yamma da ke ziyara cewa akwai wasu fannoni na musamman da za a iya ƙara haɗin kai.
Putin ya karbi bakuncin Kanal Assimi Goita a fadar Kremlin, inda suka tattauna tsawon awanni biyu, kamar yadda kafafen yaɗa labaran gwamnati na Rasha suka bayyana.
Putin ya ce dangantakar Rasha da Mali tana samun “kyakkyawan ci-gaba” duk da cewa cinikayyar ɓangarorin biyu a halin yanzu tana da “ƙaranci,” kamar yadda rahoton Kremlin ya nuna.
Daga cikin abin da yarjejeniyar ta ƙunsa akwai haɗin kai domin samar da makamashin nukiliya, kamar yadda Rashar ta bayyana.
Goita dai yana ƙara ƙulla alaƙa da Rasha ne bayan juyin mulkin da ya jagoranta a shekarar 2021, sannan ya juya wa Faransa — wadda ta raini ƙasarsu baya.
Da yake jawabi a ranar Litinin, Putin ya ce sun inganta yarjejeniyar ne, sannan suka tattaunawa hanyoyin da za su ƙara ƙulla alaƙa a “ɓangarorin ma’adinai da makamashi da agaji.”
Goita ya yi godiya ga Rasha bisa irin “karamcin” da aka masa, sannan ya nanata shirin Mali na ɗabbaƙa yarjejeniyar, waɗanda ya ce sun ƙunshi ɓangarori da dama.
Alaƙar tsaro dai na cikin muhimman abubuwan da ke tsakanin Rasha da Mali.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa
Wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Alƙalin Babbar Kotun Jihar Bayelsa, Ebiyerin Omukoro.
Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 7 na daren ranar Asabar a unguwar Ekeki, kusa da babban titin Melford Okilo a Yenagoa, babban birnin jihar.
Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a FilatoRahotanni sun bayyana cewa, mutanen sun isa a cikin mota ƙirar Hilux, sanye da baƙaƙen kaya.
Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, maharsn sun kutsa kai gidan cin abincin da alƙalin ke ciki kuma suka tilasta masa shiga motarsu.
Har zuwa yanzu, ba a san inda suka kai shi ba, kuma babu wani saƙo ko buƙatar kuɗin fansa daga masu garkuwar.
Hakazalika ba a san dalilin da ya sa suka sace shi ba.
Wannan ba shi ne karon farko da aka sace mutum a yankin ba, domin an je har gida an sace wani ɗan jarida mai suna Oyins Egrenbido.
Wasu hotuna da bidiyo da suka karaɗe shafukan sada zumunta sun nuna yadda aka kama alƙalin tare da jefa shi cikin motar ƙirar Hilux.
Har yanzu Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bayelsa, ba ta fitar da wata sanarwa ba dangane da sace alƙalin.