Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Published: 24th, June 2025 GMT
Majalisar ministocin harkokin waje ta kungiyar kasashen musulmi (OIC), ta gudanar da taronta na 51 daga ranar 21 zuwa 22 ga watan nan. Taron ya tabbatar da kokarin Sin na kare al’ummar musulmi tare da yaba wa ci gaban da aka samu na dangantaka tsakanin Sin da kasashen musulmi da kuma sa ran kara zurfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyar OIC da kasar Sin.
Da yake tsokaci kan hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jian kun, ya ce a ’yan shekarun nan, Sin da kasashen musulmi da ma kungiyar OIC, sun ci gaba da zurfafa aminci a tsakaninsu da fadada hadin gwiwarsu a bangarori daban-daban da karfafa musaya tsakanin al’ummominsu tare da samun kyawawan sakamako.
Ya ce Sin za ta ci gaba da hada hannu da kasashen da kungiyar OIC wajen raya dangantakar dake tsakaninsu. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi
Idi ya kuma yi nazari kan matakin da bangaren kiwon dabbobin kasar yake, inda yawan Shanu suka kai miliyan 20.9, Tumaki miliyan 49.1, Awakai miliyan 88.2, Kajin gidan gona kuma miliyan 258.5.
Kazalika, Maiha ya jaddada muhimmancin hadakar ta zuba hannun jari a fannin na kiwon dabbobin, wanda ya sanar da cewa; hakan zai taimaka matuka gaya wajen dakile yaduwar cututtukan da ke yi wa dabbobin illa.
A nasa jawabin, Babban Shugaban Kamfanin Ricardo Lacerda ya bayyana cewa; kasar Brazil na shirin samar da wuraren kiwon dabbobi na zamani kimanin guda 200,000 a wasu daga cikin jihohin wannan kasa, musamman don kara samar da isasshen naman Shanu.
Ya kara da cewa, kasar za kuma ta tabbatar da kokarin kara habaka bangaren kiwon Kajin gidan gona, duk dai a cikin wannan shiri.
Har ila yau, kamfanin ya sake zabo Jihar Ogun, domin tabbatar da ganin ta amfana da shirin, kazalika; kamfanin na yukurin zuba hannun jari na kimanin dala biliyan 2.5, duba da cewa; jihar ita ce ta kasance kan gaba wajen aiwatar da kiwon Kajin gidan gona a dukkanin fadin Nijeriya.
Wani mai zuba hannun jari a kamfanin Wesley Batista ne ya tabbatar da hakan, lokacin da wasu jami’an kamfaninsa, suka kai ziyara; wanda John Coumantaros ya jagoranta zuwa wurin Gwamnan Jihar Ogun Dapo Abiodun, a fadar gwamnatin jihar, da ke garin Abeokuta.
Batista ya sanar da cewa, Allah ya albarkaci kasar nan da albarkatun kasa da dama, wanda ya sanar da cewa; za su yi amfani da ilimin da suke da shi da kuma kwarewarsu a wannan bangare na kiwon dabbobi, musamman domin samun damar kara habaka tattalin arzikin kasar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp