Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
Published: 22nd, June 2025 GMT
’Yan tawayen Houthi na Yemen sun yi barazanar cewa Amurka za ta gamu da fushinsu muddin ta kai wa Iran hari a rikicin da ya ɓarke tsakaninta da Isra’ila.
’Yan tawayen sun ce za su kai wa jiragen ruwan Amurka hare-hare a Tekun Bahar Rum, idan har Washington ta yi kuskuren shiga yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar wa Iran, duk kuwa da yarjejeniya tsagaita wuta da aka cimma a baya-bayan nan.
A cikin wani faifan bidiyo, kakakin ’yan tawayen Houthi Yahya Saree ya bayyana cewa, muddin Amurka ta kai wa Iran hari ko kuma ta shiga cikin wannan rikici, mayankansu za su ƙaddamar da farmaki kan muradun Amurkar da suka haɗa da jiragen yaƙi da kuma jiragen dakon kaya da ke zirga-zirga a Tekun Bahar Rum.
Wannan barazana ta ’yan tawayen Houthi na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donad Trump ya saka wa’adin makonni biyu domin yanke shawara a game da yiwuwar shiga rikicin da ya ɓarke tsakanin Isra’ila da Iran inda aka shiga mako na biyu suna yi wa juna ruwan bama-bamai.
Sai dai kuma tuni Amurkan ta ƙaddamar da hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliyar Iran kamar yadda Shugaba Donald Trump ya bayyana a daren Asabar wayewar gari Lahadi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni
Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin, ta ce matsayin Sin dangane da batun kamfanin TikTok a bayyane yake, kuma tana jaddada aniyar gwamnatin kasar na martaba hakkokin kamfanoni yadda ya makata.
Ma’aikatar ta ce Sin na maraba da matakin gudanar da shawarwari da kamfanoni bisa doron dokokin kasuwa, ta yadda za a iya kaiwa ga shawo kan matsaloli daidai da dokokin kasar Sin, da ka’idoji, da daidaita moriyar dukkanin sassa masu takaddama.
Ma’aikatar ta ce Sin na fatan Amurka za ta dauki makamancin wannan tafarki, ta cika alkawuran da ta dauka, da samar da wata kafa ta adalci, marar nuna wariya, kuma ta bunkasa muhallin kasuwanci ga kamfanonin kasar Sin, ciki har da kamfanin TikTok, ta yadda zai ci gaba da gudanar da hada-hada a Amurka, da ingiza daidaito, da ci gaba mai inganci, da dorewar alakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp