Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
Published: 22nd, June 2025 GMT
’Yan tawayen Houthi na Yemen sun yi barazanar cewa Amurka za ta gamu da fushinsu muddin ta kai wa Iran hari a rikicin da ya ɓarke tsakaninta da Isra’ila.
’Yan tawayen sun ce za su kai wa jiragen ruwan Amurka hare-hare a Tekun Bahar Rum, idan har Washington ta yi kuskuren shiga yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar wa Iran, duk kuwa da yarjejeniya tsagaita wuta da aka cimma a baya-bayan nan.
A cikin wani faifan bidiyo, kakakin ’yan tawayen Houthi Yahya Saree ya bayyana cewa, muddin Amurka ta kai wa Iran hari ko kuma ta shiga cikin wannan rikici, mayankansu za su ƙaddamar da farmaki kan muradun Amurkar da suka haɗa da jiragen yaƙi da kuma jiragen dakon kaya da ke zirga-zirga a Tekun Bahar Rum.
Wannan barazana ta ’yan tawayen Houthi na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donad Trump ya saka wa’adin makonni biyu domin yanke shawara a game da yiwuwar shiga rikicin da ya ɓarke tsakanin Isra’ila da Iran inda aka shiga mako na biyu suna yi wa juna ruwan bama-bamai.
Sai dai kuma tuni Amurkan ta ƙaddamar da hare-hare kan wasu cibiyoyin nukiliyar Iran kamar yadda Shugaba Donald Trump ya bayyana a daren Asabar wayewar gari Lahadi.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD ya yi kiran hada karfi da karfe a bangaren kasa da kasa don karfafa tattaunawa domin ganin an yayyafa ruwa ga rikicin Isra’ila da Iran.
Wakilin, Fu Cong ya ce, yayin da rikicin yake-yaken sojoji na Isra’ila da Iran ya shiga kwana na takwas, abin bakin ciki ne ganin yadda lamarin yake janyo asarar rayukan fararen hula da dama tare da lalata kayayyakin aiki a dukkan bangarorin biyu.
Ya kara da cewa, idan har wutar rikicin ta ci gaba da ruruwa, ba kawai bangarorin biyu ne za su tafka babbar asara ba, hatta sauran kasashen yankin lamarin zai yi musu mummunar illa.
Fu Cong, ya fada wa wani taron gaggawa na kwamitin sulhun MDD cewa, matakin da Isra’ila ta dauka ya saba wa dokokin duniya da ka’idojin huldar kasa da kasa, yana kuma kawo cikas ga ‘yancin kai da tsaron kasar Iran, tare da yin kafar ungulu ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin. Kuma ba tare da wata shakka ba, kasar Sin ta yi Allah wadai da hakan. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp