A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana tsarin a matsayin wani kwakkwaran taswirar zamani da za a sa a gaba tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ganin an aiwatar da shi sosai.

 

Ya ci gaba da cewa, “A yau mun samu wani gagarumin ci gaba a tafiyarmu ta haɗin gwiwa a jihar Zamfara ta hanyar inganta fasahar zamani, ƙirƙire-ƙirƙire, da hanyoyin samun bayanai da fasahar sadarwa.

 

“Tsarin Ilimin Fasahar Zamani nna Zamfara wani tsari ne da zai amfani buƙatun al’umma na dogon lokaci don samar wa mutanenmu ƙarfin aiki da haɓaka ƙwarewarsu a cikin duniyar fasahar zamani.

 

“Kamar yadda muka sani, ilimin fasahar zamani yana da muhimmanci don samar da ayyukan yi da samar da ingantacciyar tsarin aiki. Ba zai yiwu mu rungume hannu mu bar jihar a baya ba a zamani ilimin fasahar zamani.

 

“Wannan tsarin yana da nufin samar da ilimi a bangaren fasahar zamani kan abubuwan da suma shafi – kwamfuta, ayyukan gwamnati, da kasuwanci. Tsarin yana dubi ga jihar da kowane ɗalibi zai ƙware sosai a fannin fasahar zamani, kowane ma’aikacin gwamnati zai samu fasahar zamani don gudanar da aikin sa, kuma manyan ‘yan kasuwa da ƙanana suna da ƙwarewar faɗaɗa kasuwancinsu. Mun fara shirin aiwatar da wannan hangen nesa.

“Jihar Zamfara ta haɗa gwiwa da Kamfanin Oracle domin horar da matasa 3,000 a shirin ‘Cloud 2 Computing, Artificial Intelligence, Data Science, and Database Management’. Tare da makarantar Oracle, manyan makarantunmu za su samu tallafi don yaye ɗalibai masu ƙwarewa a harkar masana’antu.

 

“An fara aiki a Cibiyar Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZIIT) da ke Gusau, wannan cibiya za ta kasance cibiyar ƙwararru ta yanki, da ke ba da ilimin kwamfuta da kuma samar da ƙirƙire-ƙirƙire a cikin gida. Muna da burin ganin mun ɗinke barakar fasahar zamani da kuma sanya Zamfara a matsayin cibiyar ilimin kwamfuta a Arewacin Nijeriya.”

 

Tun da farko, a jawabinsa na maraba sakataren gwamnatin jihar Zamfara, Malam Abubakar Nakwada, ya bayyana ƙudirin gwamnatin jihar na ganin jihar Zamfara ta kasance kan gaba wajen kawo sauyi a bangaren fasahar zamani a Arewacin Nijeriya.

 

Da take isar da saƙon fatan alheri, Sanata Ikra Aliyu Bilbis (Sanata mai wakiltar Zamfara ta tsakiya), Shugabar Kwamitin Fasahar Zamani da Tattalin Arziki na Majalisar Dattawa, ta yaba wa Zamfara kan yadda take kan gaba a lokacin da ci gaban ƙasa ya ta’allaka kan fasahar zamani. Sanatar ta ba da gudunmawar kwamfutoci 300 ga ZITDA don tallafa wa tsarin fasahar zamani a duk faɗin jihar.

A jawabinsa dangane da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani na Zamfara (ZDLF), Dokta Habib Gajam, Babban Sakatare na Hukumar Bunƙasa Fasahar Watsa Labarai ta Zamfara (ZITDA), ya bayyana tsarin a matsayin wata dabarar da ta shafi mutane da aka tsara.

 

Muhimman cibiyoyi na fasahar zamani na Gwamnatin Tarayya da aka wakilta a taron masu ruwa da tsakin sun haɗa da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC), Galaxy Backbone, Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA), Cibiyar Kuka da Tauraron Ɗan Adam, da Hukumar Kare Bayanai ta Nijeriya (NDPC).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ilimin fasahar zamani Fasahar Zamani jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi

Mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Mani Malam Mumini ya jajanta wa al’ummar karamar hukumar Gumi kan mumunan al’amuran da suka salwantar da rayukan mazauna kauyen Fas su 19 a makonnin da suka gabata.

 

Malam Mumini ya bayyana haka ne a lokacin da ya jagoranci wasu jami’an gwamnati da suka kai ziyarar jaje ga al’umma, inda ya jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa, da Majalisar Masarautar, da daukacin al’ummar Gumi.

 

Ya bayyana bala’in a matsayin mai raɗaɗi, yana mai jaddada cewa, gwamnatin jihar ta himmatu wajen magance matsalolin.

 

Mataimakin Gwamnan ya tuna cewa lamarin na farko ya faru ne a lokacin da mazauna kauyen cikin firgici kan harin da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne suka kai, suka shiga cikin wani jirgin ruwa wanda a karshe ya kife sakamakon kifewar da ya yi, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da dama.

 

Ya kuma bayyana cewa, a yayin da bala’i na biyu ya faru kwanaki bayan wata motar bus ta Homa dauke da ‘yan  daurin aure ta kutsa cikin kogin Gwalli a kan hanyar da ta wuce kan gada mai dauke da yashi, inda mutane 19 suka mutu.

 

Ya yi nuni da cewa, duk da cewa dan majalisar da ke wakiltar yankin ya gabatar da kudiri a kan munin yanayin gadar, amma har yanzu ana duba lamarin a lokacin da bala’in ya afku.

 

Mani Malam Mumini ya ce tuni gwamnatin jihar ta aike da tawagar injiniyoyi domin tantance gadar da kuma hanyoyin da suka hada da juna.

 

Wani shugaban al’umma a Gwalli ya yi kira da a kawo dauki cikin gaggawa tare da jaddada muhimman dabarun hana gadar ta ruguje nan gaba.

 

Shima da yake nasa jawabin mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara, Adamu Aliyu Gumi, ya bayyana wannan lamari a matsayin babban rashi ga al’umma, ya kuma yi kira da a gaggauta daukar mataki na gaggawa domin kaucewa afkuwar bala’o’i.

 

A yayin ziyarar, Mataimakin Gwamnan ya kuma kai gaisuwar ban girma ga Mai Martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan mai murabus, tare da jajanta masa bisa wannan al’amarin da aka samu.

 

A nasa jawabi, mai martaba Sarkin Gumi, Mai Shari’a Lawal Hassan ya bukaci gwamnatin jihar da ta hada kai da hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa NIWA domin samar wa majalisar jiragen ruwa na zamani domin rage yawaitar hadurran jiragen ruwa.

 

Mai shari’a Hassan ya koka da cewa, kwalekwalen katako na gargajiya da ake amfani da su a halin yanzu ba su da tsaro kuma suna tabarbarewa cikin sauri, suna jefa rayuka cikin hadari.

 

Sarkin ya kuma yabawa gwamnatin jihar bisa kudurin da ta dauka na magance matsalar rashin tsaro da kuma kalubalen da ke addabar jihar.

 

Tun da farko, shugaban karamar hukumar Gumi, Aminu Nuhu Falale, ya kuma bukaci a kara kaimi wajen samar da tsaro musamman a yankin Birnin Magaji, saboda karuwar hare-haren ‘yan bindiga.

 

Ya bayyana cewa, hatsarin kwale-kwale na karshe ya samo asali ne sakamakon firgici yayin da mutanen kauyen suka yi yunkurin tserewa daga hannun ‘yan bindiga, lamarin da ya kai ga kifewar kwale-kwalen.

 

COV/AMINU DALHATU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
  • Hukumar Bunkasa Ilimin Manyan Makarantu Ta Shirya Taro Na Musamman Ga Jami’anta
  • Shugabar Ma’aikata Ta Jihar Kaduna Ta Yi Kiran Amfani Da Fasahar AI.
  • Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista
  • Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya