Aminiya:
2025-06-21@17:54:37 GMT

Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Published: 21st, June 2025 GMT

Aƙalla mutum 10 ne suka rasu a daren ranar Juma’a bayan wani ɗan ƙunar baƙin wake ya kai hari da bam a wani wsjen cin abinci da ke garin Konduga, a Jihar Borno.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Daso, ya tabbatar da faruwar lamarin.

’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano

Ya ce jami’an tsaro da suka haɗa da ‘yan sanda da sojoji na gudanar da bincike domin gano haƙiƙanin abin da ya faru da kuma adadin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Ya ce, “Wani mutum ya kutsa cikin taron mutane da misalin ƙarfe 10 na dare tare da bam, wanda ya tarwatsa kansa kuma ya kashe sama da mutum 10.”

Wani masani kan ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana cewa mutum 24 ne, suka rasu a sanadin harin, inda ya ce mace ce ta kai harin ƙunar baƙin waken.

Ya ƙara da cewa fashewar ta yi tsanani wanda sai kan matar aka samu.

Bayan harin, an tura tawagar sojoji, ƙwararrun masu binciken bam na ‘yan sanda, ’yan sa-kai, da ƙungiyar CJTF zuwa wajen.

Sun yi bincike amma ba su samu bam na biyu a wajen ba.

An kwashe waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH) domin a kula da su.

An kai gawarwakin waɗanda suka rasu zuwa asibitin kuma likitoci sun tabbatar da rasuwarsu.

Makama, ya ce ana ci gaba da tantance sunayen waɗanda abin ya rutsa da su domin a miƙa gawarwakinsu ga iyalansu domin yi musu jana’iza.

Kai harin ƙunar baƙin wake na ɗaya daga cikin dabarun da ƙungiyar Boko Haram ta fara amfani da su a farko-farkon fara ta’addancinta a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɗan Ƙunar Baƙin Wake hari Wajen Cin Abinci ƙunar baƙin

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara

Al’ummar garin Kaura Namoda da ke Jihar Zamfara, sun gudanar da sallar roƙon ruwa bayan da aka shafe kwanaki ba tare da an samu ruwan sama ba.

Mutane da dama sun fara nuna damuwa saboda har yanzu babu ruwa ba, duk da cewa an shiga lokacin damina tun da daɗewa.

NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi

Wasu manoma da ke jiran ruwa domin su yi shuka sun ce har zuwa ranar Laraba sun fito domin roƙon Allah Ya saukar da ruwa.

Babban limamin garin Kaura, Malam Badamasi, ne ya jagoranci sallar.

Ya ce sun ga dacewar yin wannan addu’a ne domin tun mako biyu da suka wuce ba su samu ruwa ba a garin.

Sheikh Malam Muhammad ya yi wa jama’a wa’azi mai ratsa zuciya, inda ya tunatar da su muhimmancin komawa ga Allah da yawaita ibada a irin wannan lokaci na fari da rashin ruwa.

Daga cikin waɗanda suka halarci sallar akwai Abdul Hadi Ibrahim Mai Yadi da Kasimu Namadi.

Sun ce sun zo domin neman gafara daga Allah da fatan zai saukar da ruwa.

Sun bayyana damuwarsu da cewa mako biyu kenan ba a yi ruwa a yankinsu ba, kuma ruwan da ya zo a baya bai wadatar wajen yin shuka ba, sai kuma ya ɗauke gaba ɗaya.

Sun ce fari na ruwa babbar matsala ce ga kowa, ba wai manoma kaɗai ba.

“Wannan musiba ce da ya kamata kowa ya tashi tsaye ya roƙi Allah Ya kawo sauƙi,” in ji su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos
  • Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
  • Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila
  • Yadda manoma suka yi addu’ar roƙon ruwa a Zamfara
  • Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar Dangote