Akwai yiwuwar ƙasar Koriya ta Arewa mai ƙarfin makaman nukiliya za ta taimaka wajen gyara tashoshin nukiliyan Iran da hare-haren Amurka suka lalata da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya a Iran.

Wani masani mai suna Ankit Panda daga cibiyar zaman lafiya ta kasa da kasa ta da ke Amurka, ne ya bayyana hakan, baya Amurka ta kai hare-hare kan tashoshin nukiliya na ƙasar Iran.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito Ankit Panda, yana bayyana cewa matakin zai kawo ƙarshen irin takura da ƙasashen Yamma ke yi wa Iran.

Hakan na zuwa ne bayan da Ma’aikatar Harkokin Wajen Koriya ta Arewa ta yi tir da harin da Amurka ta kai a matsayin keta hurumin ’yanci da kuma tsaron ƙasar Iran.

NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano

Hakan na zuwa ne bayan da Ma’aikatar Harkokin Wajen Koriya ta Arewa ta yi tir da harin da Amurka ta kai a matsayin keta hurumin ’yanci da kuma tsaron ƙasar Iran.

Ta bayyana cewa, “Amurka da Isra’ila su ne kanwa uwar gani a rikici a yankin Gabas ta Tsakiya, sakamakon yake-yake da ƙoƙarin Isra’ila na faɗaɗa girman ƙasarta, tare sa smaun goyon bayan ƙasashen Yamma.

“Ya kamata al’ummomin duniya masu goyon bayan adalci su fito da murya ɗaya aula’anci wannan abin da Amurka da Isra’ila ke yi, kuma su taka musu burki,” in ji sanarwar da kamfanin dillancin labarai na Koriya ta Arewa (KCNA) ya ruwaito.

Ƙawancen soji tsakanin Iran da Koriya ta Arewa ta jima, kuma ana zargin ta taimaka musu wajen haɗawa da musayar makamai masu linzami masu gudun walƙilya masu cin dogon zango.

Ankit ya ce ba lallai ne Koriya ta Arewa ta taimaka wa Iran wurin ginawa ko hanzarta ƙera makaman nukiliya ba, domin gudun kada makaman su je Amurka. Idan hakan ya faru, Amurka na iya gano lagon fasahar makaman Koriya ta Arewar.

Amma dai akwai yiwuwar Koriya ta Arewar za ta iya, lura da yadda ke da ƙwarewa wajen fasahar makamai da kuma yadda a baya da yawaita taimako ta wannan bangare ga Rasha, wata babbar ƙawar Iran.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila Koriya ta Arewa nukiliya Koriya ta Arewa ta

এছাড়াও পড়ুন:

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

Idris, wanda shi ne ya jagoranci zaman, ya bayyana irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Babban Hafsan Tsaro da sauran Hafsoshin Sojin a matsayin mai tabbataccen tasiri da gamsasshen sakamako.

 

Ya ce: “Abin da muka gani ba wai kawai daƙile waɗannan barazanar ba ne, sai dai ma sake karɓe sararin ƙasar mu, da tunanin jama’a, da kuma a matakin aiki. Yanzu ‘yan Nijeriya za su iya tabbatar da cewa manyan hanyoyin mu sun fi samun tsaro ƙwarai idan aka kwatanta da ‘yan shekarun baya.”

 

Ya lissafa nasarorin da rundunonin sojin Nijeriya suka samu a sassa daban-daban na ƙasar nan, ciki har da yankin Arewa-maso-gabas da gaɓar teku.

“Daga nasarar ragargaza sansanonin Boko Haram da ISWAP a Arewa-maso-Gabas, zuwa irin gagarumin farmakin da aka kai kan maɓoyar ‘yan bindiga a Arewa-maso-Yamma da Arewa-ta-Tsakiya; daga ingantaccen sintirin da sojin ruwa ke yi wanda ya rage yawan satar ɗanyen mai da rushe haramtattun matatun mai; zuwa luguden wutar sama da ba ya ƙarewa wanda ya tarwatsa hanyoyin sufuri da ɗaukar kaya na miyagun mutane — sakamakon da aka samu ba kawai abin burgewa ba ne, har ma abin kwantar da hankali ne.”

 

Ministan ya kuma jaddada muhimmancin rawar da kafafen yaɗa labarai suke takawa wajen gina ƙasa, yana mai roƙon su da su tallafa wa ƙoƙarin da rundunonin tsaro suke yi ta hanyar yaɗa nasarorin da suke samu.

 

Ya ce: “Ya kamata kafafen yaɗa labarai su riƙa bada rahoto ba kawai kan abin da ya zama ba daidai ba, har ma da abin da ake yi daidai. Ku riƙa hasko irin sadaukarwar da dakarun mu suke yi. Ku bada labaran cigaba da ake samu. Ku daidaita suka da cikakken bayani. Wannan shi ne ainihin aikin jarida bisa ƙwarewa.”

 

Ya bada tabbacin cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da tallafa wa rundunar soji ba kawai da kayan aiki kaɗai ba har ma da tsare-tsaren dabarun da za su inganta tattara bayanan sirri, haɗin gwiwar hukumomi, da walwalar ma’aikata.

 

Ya yaba wa Hafsoshin Sojin bisa shugabancin su na kishin ƙasa da samar da sakamako mai tasiri.

 

“Kun dawo da fata, kun ceci rayuka, kun kare martabar ƙasar mu, kuma fiye da komai ma, kun tunatar da mu ma’anar yi wa ƙasa hidima,” inji shi.

 

Ya kuma buƙaci kafafen watsa labarai da sauran masu ruwa da tsaki da su riƙa haska irin nasarorin da ake samu, yana mai cewa hakan yana da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa gwiwar jami’an tsaro.

 

“Ku lura da cigaban da ake samu kuma ku faɗaɗa yaɗuwar sa. Wannan na da matuƙar amfani ga ɗimbin dakarun mu da ke aiki dare da rana don kare ƙasar nan da samar da yanayin da duk ‘yan Nijeriya za su iya rayuwa, su yi aiki, su bunƙasa.”

 

Taron ya samu halartar Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, wanda Manjo Janar A.T. Jibrin (ritaya) ya wakilta; da Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa; da Manajan Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN), Malam Ali M. Ali; da Babban Daraktan Hukumar Gidajen Rediyon Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; da Babban Daraktan Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; da Shugaban da Shugaban Majalisar Ƙungiyar Masana Harkokin Yaɗa Labarai ta Nijeriya (NIPR), Dakta Ike Neliaku; da wakilan Hafsoshin Soji, da manyan shugabannin kafafen yaɗa labarai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz
  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya
  • Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa