Mahaifiyar Babban Editan jaridar Daily Trust ta rasu
Published: 23rd, June 2025 GMT
Allah Ya yi wa mahaifiyar Babban Editan Jaridar Daily Trust, Hamza Idris rasuwa.
Kaninsa, mai suna Aminu Idris, ya bayyana cewa a safiyar Litinin ne Allah Ya yi wa mahaifiyar Babban Editan, Hajiya Rabi (Umma) cikawa bayan gajeruwar jinya a Jihar Kano.
Za a gudanar da jana’izarta kamar yadda addinin Musulunci ya ranar a Layin Ɗorawar ’Yan Kifi da ke unguwar, Rijiyar Zaki, Kano.
Daga nan za a kai ya maƙabartar Walid Mai Zage da ke Kofar Mazugal.
Muna roƙon Allah Ya yi mata rahama, Ya ba wa dangi haƙurin rashin da kuma dangana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babban Editan Jaridar Daily Trust mahaifiyar
এছাড়াও পড়ুন:
Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
Ana fargabar mutum biyar sun mutu a sakamakon tashin bom a Jihar Kano a ranar Asabar.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ba bayyana cewa bom ɗin soja ne ya tashi.
Kwamishinan ya ce akwai yiwuwar kuskure wurin safara ko kuma wurin kula da abin fashewan.
Ya bayyana haka ne a yayin ziyarar gani da ido da ya kai wurin da abin ta tashi.