Gonar ta ‘AA Dibine Agro’, ta kasance a yankin Pasali Karshi da ke cikin karamar Hukumar Karu a Jihar Nasarawa.

Kazalika, kudirin shi ne; nomawa da kuma samar da isasshen Filanten din da za a rika kai wa har zuwa babban birnin tarayya  Abuja, domin sayar da shi.

A cewar tasa, abin da gonar ke son cimma shi ne, taimaka wa fannin aikin noma na tarayyar kasar nan, wanda hakan zai kuma kara tallafawa wajen kara samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa tare da samar da wadataccen abinci.

Sai dai, ya bayyana cewa; rashin kudaden da za a yi amfani da su wajen cimma wannan manufa, su ne babban cikas.

Gonar, wadda aka samar da ita a zagayen Katangu, domin kiwon dabbobi, na matukar fama da karancin ruwa da ya yi sanadiyyar dakatar da gudanar da dukkanin wasu ayyuka da ake yi a cikinta.

Bugu da kari, rashin samar da hanya; wadda za a rika amfani da ita wajen safarar amfanin gonar da aka girbe, na daya daga cikin kalubalen da gonar ke fuskanta.

Amma duk da irin wadannan matsaloli da gonar ta ‘AA Dibine’ ke fuskanta, ta tanadi wasu muhimman manya-manyan shirye-shiye.

Daga cikin shirye-shiyen sun hada da; burin samar da wuraren kiwon dabbobi da kiwon Kajin gidan gona da wuraren kiwon Kifi da kuma sarrafa abincin dabbobi, wanda hakan zai taimaka wajen habaka tattalin arzikin yankin tare da samar da ayyukan yi da kuma kara bunkasa noma.

kungiyar ta COMAFAS, ta fi mayar da hankali ne wajen tallafa wa manoma da kuma kara habaka fannin aikin noma.

A cewar Dakta Maduka, kungiyar ta amince da yarjejeniyar ce, duba da cewa; ta lura da manufar da gonar ta ‘AA Dibine Farm Limited’, ta sanya a gaba, musamman domin tsamo gonar daga cikin babban kalubalen da take fuskanta tare kuma da samun damar cimma burin da ta sanya a gaba.

Ya kara da cewa, hadakar za kuma ta taimaka wajen samar da ilimi da masu zuba hannun jari da kuma samun tallafin kudi ga gonar. Haka zalika, kudin zai taimaka, wajen sama wa gonar kayan aikin da take bukata da kuma samar da hanyar yin jigilar amfanin gonar da aka shuka.

Sauran daukin da hadakar za ta samar, sun hada da horo da kuma tabbatar da shugabanci nagari da sauran makamantansu.

Dakta Maduka, ya kuma bayar ta tabbacin cewa; ta hanyar jawo sauran abokan hadaka cikin wannan aiki, za a iya noman wannan Filanten mai matukar tarin yawa a gonar, duba da cewa; yankin na da yanayi mai kyau na yin noma da ake bukata, inda kuma hakan zai kara taimakawa wajen samar da ayyukan yi.

Kazalika, ya bayyana cewa; hadakar za kuma ta kara taimakawa wajen kara habaka tattalin arzikin yankin tare da samar da wadataccen abinci yadda ya kamata. 

A cewar tasa, gonar ta ‘AA Dibine Farm Limited’, za ta kasance mai aiki da kayan noma na zamani a tsakanin sauran gonakin da ke fadin kasar nan, ta hanyar taimakon kungiyar ta COMAFAS.

Har ila yau, daukacin masu kulla wannan yarjejeniya, sun amince da kara habaka wannan bangare na noma a dukkanin fadin Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ayaba

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa

Daga Usman Muhammad Zaria

Gidauniyar Tunawa da Marigayi Sir Ahmadu Bello (ABMF) ta yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa sauƙin kai, tawali’u da jajircewarsa wajen ci gaban Jihar Jigawa.

Shugaban Kwamitin Amintattu na Gidauniyar kuma tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dr. Mu’azu Babangida Aliyu ne ya yi wannan yabon yayin da ya jagoranci tawaga zuwa gaisuwar ban girma a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse.

Ya ce salon jagoranci na Gwamna Namadi na ɗauke da ƙima da marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato, ya shahara da su, musamman tsari, girmama jama’a da shugabanci na gaskiya da rikon amana.

Dr. Aliyu ya yi kira ga shugabannin Arewa su rungumi jagoranci da ke maida hankali kan al’umma, tare da fifita ilimi a matsayin tubalin cigaba.

Ya kuma sanar da cewa Jihar Jigawa ce za ta karbi bakuncin taron gidauniyar na shekarar 2026, wanda zai ƙunshi laccoci, shirye-shiryen wayar da kan jama’a da bada lambar yabo.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya gode wa Gidauniyar bisa wannan yabo da kuma zaɓar Jigawa don karɓar taron na 2026.

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba da bin sawun Sardauna ta hanyar shugabanci na gaskiya, tsare-tsaren jin daɗin jama’a da kuma zuba jari a fannin ilimi.

Ya tabbatar da cikakken goyon baya wajen shirya taron 2026 cikin nasara.

Tawagar ta haɗa da Madakin Zazzau, Malam Muhammad Munir Ja’afaru, da wasu jami’an Gidauniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu!
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Najeriya: Ta Sake Jaddada Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu