Mai bai wa Gwamna Uba Sani shawara kan harkokin kwadago, Adamu Samaila ne ya shaida wa wakilinmu cewa; nan bad a jimawa ba gwamnati za ta karbi rahotan tantance ma’aikatan da kuma yadda za a daidata albashin nasu.

Samaila ya kara da cewa, “A mako mai zuwa ne za mu gana da wanda yake kula da aikin tantancewar, domin samun sakamakon rahoton albashin ma’aikatan.

Zamfara: Ba A Aiwatar Da Biyan Dari Bisa Dari Ba

A Jihar Zamfara, gwamnati ba ta aiwatar da fara biyan sabon mafi karancin albashin ga ma’aikatanta ba. Guda daga cikin manyan jami’an gwamnatin da ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa wakilinmu cewa; mafi karancin albashin, zai fi mayar da hankali ne a kan ma’aikatan da ke mataki na uku zuwa mataki na bakwai, wajen biyan cikakken albashin na Naira 70,000, sabanin wadanda ke kan mataki na 8 zuwa sama.

Shugaban kungiyar malamai na Nijeriya (NUT), Yahaya Mafara ya bayyana cewa; ana kan yin gyara kan batun biyan wannan albashi na ma’aikata.  

Nasarawa: Na Biyan Kashi 40 Cikin 100

A Jihar Nasarawa, har yanzu ma’aikatan kananan hukumomi da malaman makarantun gaba da sakandare, bas u samu cikakken wannan mafi karancin albashi na Naira 70,000 ba. Shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Nijeriya (NULGE) na jihar, Kwamared Adamu Sharhabilu, ya shaida wa LEADERSHIP cewa; a halin yanzu ma’aikata na samun kashi 40 cikin 100 na karin mafi karancin albashin, ya kuma bayyana fatansa na fara aiwatar da biyan cikakken albashin na Naira 70,000 daga nan zuwa karshen watan Yuni.

Haka zalika, ya kuma alakanta wannan gazawar da batun kason kudaden kananan hukumomi da ake yankewa daga asusun gwamnatin tarayya.

Sharhabilu ya bayyana cewa, “Ka san karamar hukuma, ba kamar jiha ba ce, ana cire kashi biyar cikin dari na Sarakuna, kashi daya na horar da hukumar kula da ma’aikatan kananan hukumomi, kashi daya na babban mai bincike, kashi daya na ma’aikatar kananan hukumomi da kuma kashi daya na hukumomin lafiya.

Don haka, abin da ya yi saura bayan an cire wadannan, ba zai isa a biya wannan mafi karancin albashi ba. Amma, mun gana da hukumomin da abin ya shafa kan lamarin tare da dagewa wajen ganin an biya cikakken wannan mafi karancin albashi daga nan zuwa karshen watan Yuni”, in ji shi. 

Borno: Ana Ci Gaba Da Tantance Ma’aikata

Yayin da ake aiwatar da biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 ga wasu ma’aikatan Jihar Borno, gwamnatin na gudanar da wani atisayen tantance ma’aikata na kwarai a kananan hukumomi.

A cewar kungiyar NUT reshen Jihar Borno, malamai a matakin jihad a kananan hukumomi na karbar mafi karancin albashi na Naira 70,000, sai dai sauran nau’o’in malaman da aka sanya wa horo na tsawon wata uku, daga nan ne za su fara karbar mafi karancin albashin.

Shugaban kungiyar ta NUT, Comrade Yusuf Inuwa, ya roki a kara wa kafatanin ma’aikatan da suka fito daga kananan hukumomi 27 na jihar, inda ya ce; har yanzu ma’aikatan kananan hukumomin ba su ci gajiyar karin mafi karancin albashin ba.

Yobe: Har Yanzu Ana Bin Tsohon Albashi

Wasu malaman makaranta a Jihar Yobe sun yi ikrarin cewa, ba a biya su mafi karancin albashi na Naira 30,000 da kuma wannan na Naira 70,000 ba. Har ila yau, sun dora alhakin hakan; kan shugabannin kananan hukumomi, wadanda suka dage kan cewa; ba za su iya biyan tsoffi da kuma sabon mafi karancin albashin ba, ba tare da korar wasu daga cikin malamai da ma’aikatan kananan hukumomi ba.

Don haka, shugabannin kungiyar NUT da ma’aikatan kananan hukumomi, sun yi kira ga Gwamna Mai Mala Buni, da ya tabbata ya aiwatar da biyan wannan mafi karancin albashi na Naira 70,000.  

Ogun: An Fara Biyan Mafi karancin Albashin Tun 2024

A Jihar Ogun, kungiyar hadin gwiwa (JNC) kan biyan sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 ga ma’aikata ta tabbatar da cewa; Gwamnatin Gwamna Prince Dapo Abiodun, tun shekarar 2024 ta cika alkawarin da ta dauka na biyan sabon mafi karancin albashi.

kungiyar hadin gwiwar, wadda ta hada da NLC da TUC, ta bayyana cewa; ma’aikatan Jihar Ogun ba su da wata matsala da gwamnatin jihar, dangane da batun wannan sabon mafi karancin albashi, sai dai kawai batun da suka shafi jin dadi da walwalar ma’aikata da sauran makamantansu.  

Ribas: Naira 85,000 Ake Biya A Matsayin Mafi karancin Albashi

A Jihar Ribas, malaman makaratun firamare da na sakandiren gwamnati da kuma ma’aikatan kananan hukumomi, na karbar Naira 85,000 a matsayin mafi karancin albashin da gwamnan da aka dakatar, Sir Siminalayi Fubara ya amince ya biya.

Da yake tabbatar da hakan ga LEADERSHIP, shugaban kungiyar NUT Dakta Collins Echikpu ya ce; malamai a jihar sun fara karbar sabon mafi karancin albashin.

Filato: Ta Fara Biya Tun 2024

Shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi ta kasa (NULGE) reshen Jihar Filato, Kwamared Yohana Makwin ya tabbatar da cewa; gwamnatin jihar ta fara aiwatar da mafi karancin albashi na Naira 70,000 ga ma’aikatan kananan hukumomi, tun a watan Disambar 2024. 

Makwin, ya shaida wa LEADERSHIP a Jos cewa; gwamnatin jihar na ci gaba da biyan sabon mafi karancin albashin. Haka nan, takwaransa Kwamared Kefas Nanpan, ya sake tabbatar da al’amarin.  

Katsina: Ita Ma Ta Bi Sahun Biyan Naira 70,000

A Jihar Katsina, shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomin Nijeriya (NULGE), Kwamared Nasiru Wada Mai Adua, ya yaba wa Gwamna Umaru Dikko Radda, bisa jajircewarsa na kyautatawa ma’aikata

Ya yaba wa gwamnan, bisa aiwatar da biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 da kuma tabbatar da biyan kudaden giratuti na ma’aikatan da suka yi ritaya, tun daga watan Disambar 2024. Nasiru, ya bayyana hakan a matsayin sauki ga ma’aikata da kuma ‘yan fansho a jihar.

Kwara: Na Biyan Albashin Bai-daya

Ana biyan ma’akatan kananan hukumomi da malamai mafi karancin albashi na Naira 70,000 a Jihar Kwara.

Kakakin kungiyar kananan hukumomin Nijeriya (ALGON), sannan kuma Shugaban karamar Hukumar Ifelodun, Barista Femi Yusuf, ya tabbatar da hakan yayin wata tattaunawa da LEADERSHIP a Ilorin.   

Ya bayyana cewa, Jihar Kwara; jiha c eta musamman wadda a koda-yaushe kananan hukumomi da jiha ke tafiya bai-daya, wajen aiwatar da tsarin jin dadin ma’aikata. Shugaban kungiyar NLC na jihar, Kwamared Murtala Olayinka, ya tabbatar da wannan batu na Kakakin kungiyar ta ALGON. 

Anambra: Na Biyan 82,000 A Matsayin Mafi karancin Albashin Ma’aikata

A Jihar Anambara, ma’aikatan kananan hukumomi na karbar Naira 82,000 a matsayin sabon mafi karancin albashin ma’aikata. Dukkanninsu, shugaban kungiyar NLC Kwamared Humphrey Nwafor da kuma shugaban kungiyar NULGE, Kwamared Chudi Orakwe, sun tabbatar da biyan kudin a wata tattaunawa da suka yi da LEADERSHIP. 

Imo: Malamai Da Ma’aikatan kananan Hukumomi Sun Dara

Gwamnan Jihar Imo, Gwamna Hope Uzodimma; ya aiwatar da biyan Naira 70,000 a matsayin sabon mafi karancin albashin ma’aikata da malaman makaranta. Babban sakataren yada labaran gwamnan, Oguwuike Nwachuku ya ce; hakan ya yi daidai da umarnin da gwamnatin tarayya ta bayar. Da yake zantatawa da LEADERSHIP, shugaban kungiyar ta NULGE na jihar, Kwamared Charles Okere, ya yaba wa gwamnan; bisa aiwatar da biyan sabon mafi karancin albashin na Naira 70,000 ga ma’aikatan kananan hukumomi.   

Ondo: An Cika Alkawari

A Jihar Ondo, LEADERSHIP ta tattaro cewa; ana biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 ga kowane bangare na ma’aikata. Wani jami’in kungiyar NULGE day a nemi sakaye sunansa, ya bayyana cewa; gwamnan ya cika alkarin day a yi wa ma’aikata, dangane da mafi karancin albashi. 

Edo: Albashi Ya karu Zuwa Naira 75,000

A Jihar Ido, ma’aikata a halin yanzu na karbar Naira 70,000 a matsayin sabon mafi karancin albashi, wadda tsohuwar gwamnatin Gwamna Godwin Obaseki ta gabatar. A yayin bikin ranar Mayun 2025, Gwamna Monday Okpebholo ya kara albashin zuwa Naira 75,000 tare kuma da alkawarin ci gaba da inganta jin dadin ma’aikatan jihar. Sai dai, shugaban kungiyar malamai NUT na jihar, Bernard Ajobiewe ya ce; har yanzu ba a kamma shirye-shiryen fara biyan ba.

Akwa Ibom: Uniform Template

Shugaban kungiyar ma’aikata na jihar, Kwamared Sunny James, ya tabbatar da cewa; ma’aikatan kananan hukumomi, ba su fuskanci matsala kan batun mafi karancin albashin na Naira 70,000 ba. Ya alakanta batun samun daidaito na biyan ma’aikatan masana’antu da jihohi da kuma kananan hukumomi. Da yake jawabi a Uyo, ya kara da cewa; Gwamna Umo Eno, ya kara albashi zuwa Naira 82,000.

Kano: An Aiwatar Da Sabon Mafi karancin Albashi

Ma’aikatan kananan hukumomi da malaman firamare na karbar Naira 70,000 a matsayin sabon mafi karancin albashi. Wata malama da ke mataki na 10 ta bayyana cewa, albashinta yanzu ya koma Naira 82,000. 

Ekiti: Ta Na Biyan Dukkannin Ma’aikata Naira 79,000 A Matsayin Mafi karancin Albashi

Ana biyan dukkanin ma’aikatan kananan hukumomi Naira 79,000. Shugaban NULGE na jihar, Kwamared Oluseyi Olatunde ya ce; an fara aiwatar da biyan tun a watan Junairun 2025.

Takwaransa na kungiyar NUT, Kwamared Adedeji Egbeyemi, ya tabbatar da hakan; inda ya bayyana cewa, an fara biyan ma’aikatan tun a shekarar da ta gabata.  

Delta: Ta Fara Biya Tun Shekarar 2024

An fara biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 ga ma’aikatan gwamnati, musamman malaman makaranta tun a watan Nuwamban 2024.

Sakataren kungiyar NUT na jihar, Kwamared Dan Basime, ya bayyana jin dadinsa da yadda aka gaggauta biyan. Kwaminan ilimin firamare, Dakta Kingsley Ashibogwu, ya bad a tabbacin ci gaba da biyan. A baya dai, Gwamna Sheriff Oborebwori, ya umarci dukkanin shugabannin kananan hukumomi 25 tare da kungiyoyin ALGON, NUT da kuma NULGE, da tabbata sun aiwatar da biyan sabon tsarin mafi karancin albashin.

Niger: Ta Aiwatar Da Fara Biyan Naira 80,000

Gwamna Mohammed Umaru Bago, ya sanar da biyan Naira 80,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan kananan hukumomi da kuma malaman makaranta.

Shugaban kungiyar NLC kuma babban jami’in kungiyar NULGE, Kwamared Idris Lafene, ya tabbatar da cewa; an fara aiwatar da biyan wannan sabon mafi karancin albashi ga dukkanin ma’aikatan gwamnati.

Enugu: An Fara Biyan Naira 80,000 

Gwamnatin Gwamna Peter Mbah, ta aiwatar da biyan sabon mafi karancin albashi na Naira 80,000 ga dukkanin daukacin ma’aikatanta. Shugaban kungiyar NUT, Kwamared Theophilus Nweke, ya tabbatar da cewa; babu wani banbanci wajen aiwatar da fara biyan wannan sabon tsarin albashi.

Osun: Tana Biya Duk Da Rike ata Kudade Da Ake Yi

Duk da hana kudaden kananan hukumomi daga asusun tarayya, gwamnatin jihar ta ci gaba da biyan albashi.

Shugaban kungiyar NULGE na jihar, Dakta Bayo ya shaida wa LEADERSHIP cewa; takun-saka tsakanin shugabannin kansiloli, bai shafi batun biyan ma’aikata albashi ba. Dukkanin ma’aikata, na karbar sabon mafi karancin albashin Gwamnatin Ademola Adeleke na Naira 75,558.24 tun daga watan Junairun 2025. 

Amma, duk da fara biyan wannan mafi karancin albashi na 70,000, har yanzu ana ci gaba da fuskantar matsin rayuwa a fadin wannan kasa, sakamakon matsalar tsadar kayan abinci da sauran kayan masarufi.

Wasu na ganin, ko da 100,000 aka fara biya a matsayin sabon mafi karancin albashi, mafi yawan kananan ma’aikata; ba za su iya daukar nauyin iyalansu yadda ya kamata, duba da yadda tattalin arzikin kasar ya tabarbare, komai ya yi tsada.

Sanin kowa ne, yanzu haka; wannan 70,000, ba za ta taba iya saya wa magidanci buhun shinkafa daya ba, ban da batun kula da harkar lafiya, cefane na yau da kullum, wutar lantarki, ruwan sha, sabulun wanka da wanki, kudaden zirga-zirga, biyan kudin makarantar yara da sauran dawainiya ta yau da kullum.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Matsin Rayuwa Nijeriya biyan mafi karancin albashi na Naira 70 000 000 a matsayin sabon mafi karancin albashi mafi karancin albashi na Naira 70 000 ga 000 a matsayin mafi karancin albashi biyan sabon mafi karancin albashi sabon mafi karancin albashin na Naira 70 000 ga ma aikata wannan mafi karancin albashi Shugaban kungiyar ma aikata albashin na Naira 70 000 Mafi karancin Albashi shugaban kungiyar ma Biyan Mafi karancin ya tabbatar da cewa malaman makaranta aiwatar da biyan Ya bayyana cewa fara aiwatar da na karbar Naira gwamnatin jihar ya bayyana cewa Naira 70 000 A Naira 70 000 a da biyan sabon kungiyar NULGE An Fara Biyan An fara biyan kashi daya na da fara biyan fara biyan ma Da Fara Biyan an fara biyan biyan wannan ya shaida wa Naira 80 000 kungiyar NUT in kungiyar biyan Naira Biyan Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

Sanarwar ta ce: “Ma’aikatar Harkokin Waje na sanar da jama’a cewa, sakamakon rikicin da ke kara kamari tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin Tarayya tana shirin karshe na kwaso ‘yan Nijeriya da suka maƙale a wadannan kasashe.

“Saboda haka, ana shawartar dukkanin ‘yan Nijeriya da abin ya shafa da su kiyaye matakan tsaro da kuma tuntubar ofishin jakadanci mafi kusa domin yin rijista da samun karin umarni.”

Baya ga haka, Gwamnatin Tarayya ta sake kira da a dakatar da fada tsakanin Isra’ila da Iran, tare da bukatar bangarorin su rungumi tattaunawa, su mutunta dokokin kare hakkin dan Adam na duniya, kuma su bai wa rayuwar fararen hula muhimmanci.

Ma’aikatar ta jaddada cewa Nijeriya na goyon bayan hanyoyin warware rikici ta hanyar lumana da kuma tallafa wa zaman lafiya a yankuna da duniya baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila
  • Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici
  • Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • Nijeriya za ta fara fitar ta tataccen mai zuwa Asia — Matatar Dangote
  • Ma’aikatan Kwalejin Ilimi ta jihar Kaduna za su tsunduma yajin aiki