Aminiya:
2025-07-12@16:50:16 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya

Published: 21st, June 2025 GMT

Wakilin ƙasar Iran ya isa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya domin halartar taron Ƙungiyar Haɗin kan Kasashen Musulmi (OIC) a ranar Asabar.

Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito cewa, a yayin taron Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, zai gana da jami’an diflomasiyya na ƙasashen Larabawa don tattauna batun rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin ƙasarsa da Isra’ila.

Kimanin jami’an diflomasiyya 40 ne ake sa ran za su halarci taron a daidai lokacin da Isra’ila da Iran ke ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami.

“Ministan harkokin wajen ya isa Istanbul a safiyar yau domin halartar taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan Musulunci,” in ji Tasnim.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia

Wannan ziyarar ta zo ne bayan da Ministan ya gana da takwarorinsa daga Biritaniya, Faransa, da Jamus a Geneva a ranar Juma’a.

A cewar kamfanin dillancin labaran, “A wannan taron, bisa shawarar Iran, za a tattauna batun harin da gwamnatin Isra’ila ta kai wa kasarmu musamman,” in ji Araghchi.

Isra’ila ta fara farmakinta ne a safiyar 13 ga watan Yuni, tana mai cewa Iran tana dab da ƙera makaman nukiliya.

Wannan ya haifar da martani nan take daga Tehran, a rikici mafi mubi da aka taɓa fuskanta tsakanin kasashen biyu masu zaman doya da manja.

Tun da farko a ranar Juma’a, Araghchi ya bayyana cewa Iran a shirye take ta “sake duba harkokin diflomasiyya” idan har “aka dakatar da hare-haren Isra’ila.”

Ana sa ran ministocin ƙasashen Larabawa za su fitar da sanarwa bayan ganawarsu, in ji kamfanin dillancin labarai na ƙasar Turkiyya Anadolu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila Ƙasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

A yau Alhamis ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon taya murnar bude taron ministocin kasa da kasa na tattaunawa kan wayewar kan bil Adam.

A cikin sakonsa, Xi ya jadadda niyyar Sin na hadin gwiwa da kasashe daban-daban, don tabbatar da shawarar raya wayewar kan duniya bisa tushen adalci, da koyi da juna, da mu’ammala da yin hakuri da juna, ta yadda za a kafa nagartaccen tsarin mu’amalar wayewar kan bil Adam a duniya, matakin da zai gaggauta bunkasa wayewar kan bil Adam, da bunkasar duniya cikin lumana.

Shugaba Xi ya kuma yi fatan mahalarta taron za su zurfafa mu’amala, da cimma matsaya daya, da taka rawar ganin wajen karfafa cudanyar al’ummun kasa da kasa, da hadin gwiwar al’adu na kasashen daban-daban. (Amina Xu)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu