Aminiya:
2025-09-20@11:05:28 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya

Published: 21st, June 2025 GMT

Wakilin ƙasar Iran ya isa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya domin halartar taron Ƙungiyar Haɗin kan Kasashen Musulmi (OIC) a ranar Asabar.

Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito cewa, a yayin taron Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, zai gana da jami’an diflomasiyya na ƙasashen Larabawa don tattauna batun rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin ƙasarsa da Isra’ila.

Kimanin jami’an diflomasiyya 40 ne ake sa ran za su halarci taron a daidai lokacin da Isra’ila da Iran ke ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami.

“Ministan harkokin wajen ya isa Istanbul a safiyar yau domin halartar taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan Musulunci,” in ji Tasnim.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia

Wannan ziyarar ta zo ne bayan da Ministan ya gana da takwarorinsa daga Biritaniya, Faransa, da Jamus a Geneva a ranar Juma’a.

A cewar kamfanin dillancin labaran, “A wannan taron, bisa shawarar Iran, za a tattauna batun harin da gwamnatin Isra’ila ta kai wa kasarmu musamman,” in ji Araghchi.

Isra’ila ta fara farmakinta ne a safiyar 13 ga watan Yuni, tana mai cewa Iran tana dab da ƙera makaman nukiliya.

Wannan ya haifar da martani nan take daga Tehran, a rikici mafi mubi da aka taɓa fuskanta tsakanin kasashen biyu masu zaman doya da manja.

Tun da farko a ranar Juma’a, Araghchi ya bayyana cewa Iran a shirye take ta “sake duba harkokin diflomasiyya” idan har “aka dakatar da hare-haren Isra’ila.”

Ana sa ran ministocin ƙasashen Larabawa za su fitar da sanarwa bayan ganawarsu, in ji kamfanin dillancin labarai na ƙasar Turkiyya Anadolu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila Ƙasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

Dong Jun ya bayyana haka ne yayin taruka daban-daban da ya yi da shugabannin rundunonin tsaro na kasashen Malaysia da Cambodia da Myanmar da Namibia da Rwanda da Senegal, wadanda dukkansu ke birnin Beijing domin halartar taron dandalin tsaro na Xiangshan karo na 12.

Da yake yi musu maraba, Dong Jun ya ce taron na wannan karo na da matukar muhimmanci ga tarihi.

Ya kara da cewa, a shirye rundunar sojin Sin ta ke ta ci gaba da raya dadaddiyar abotar dake tsakaninta da dukkan bangarori wajen karfafa tuntubar juna da hadin gwiwa kan tsaro, da hada hannu wajen tunkarar hadura da kalubale a duniya.

Yayin tarukan, dukkan ministocin tsaron kasa da kasa da suka halarci taron, sun bayyana kudurinsu na karfafa hadin gwiwar soji da kasar Sin.

(Amna Xu/Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada ‘Yancin Kasar Na Mayar Da Martani Kan Sabawa Doka
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Mayar Da Martani Kan Zargin Shugaban Kasar Faransa
  • An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
  • Kungiyar Tarayyar Turai EU Ta Mika Bukatunta Ga Kasar Iran.
  • An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Iran Ta Sauke Hakkin Da Ya Hau Kanta Sauran Bangaren Turai
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Ce: Maso Goyon Bayan Isra’ila Suna Da Hannu A Laifukanta
  • Harin Makami Mai Linzami Yemen Ya Tilastawa Jirgin Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Saukar Gaggawa
  • Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya