Aminiya:
2025-08-06@04:33:03 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran ya isa taron Kungiyar OIC a Turkiyya

Published: 21st, June 2025 GMT

Wakilin ƙasar Iran ya isa birnin Santanbul na ƙasar Turkiyya domin halartar taron Ƙungiyar Haɗin kan Kasashen Musulmi (OIC) a ranar Asabar.

Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito cewa, a yayin taron Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, zai gana da jami’an diflomasiyya na ƙasashen Larabawa don tattauna batun rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin ƙasarsa da Isra’ila.

Kimanin jami’an diflomasiyya 40 ne ake sa ran za su halarci taron a daidai lokacin da Isra’ila da Iran ke ci gaba da musayar hare-haren makamai masu linzami.

“Ministan harkokin wajen ya isa Istanbul a safiyar yau domin halartar taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan Musulunci,” in ji Tasnim.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia

Wannan ziyarar ta zo ne bayan da Ministan ya gana da takwarorinsa daga Biritaniya, Faransa, da Jamus a Geneva a ranar Juma’a.

A cewar kamfanin dillancin labaran, “A wannan taron, bisa shawarar Iran, za a tattauna batun harin da gwamnatin Isra’ila ta kai wa kasarmu musamman,” in ji Araghchi.

Isra’ila ta fara farmakinta ne a safiyar 13 ga watan Yuni, tana mai cewa Iran tana dab da ƙera makaman nukiliya.

Wannan ya haifar da martani nan take daga Tehran, a rikici mafi mubi da aka taɓa fuskanta tsakanin kasashen biyu masu zaman doya da manja.

Tun da farko a ranar Juma’a, Araghchi ya bayyana cewa Iran a shirye take ta “sake duba harkokin diflomasiyya” idan har “aka dakatar da hare-haren Isra’ila.”

Ana sa ran ministocin ƙasashen Larabawa za su fitar da sanarwa bayan ganawarsu, in ji kamfanin dillancin labarai na ƙasar Turkiyya Anadolu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila Ƙasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Mu daina zagin malaman addini idan muna son zaman lafiya — Uba Sani

Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani, ya gargadi ’yan siyasa da masu amfani da kafafen sada zumunta da su daina zagin malaman addini da a yanzu ya zama ruwan dare a ƙasar nan.

Gwamnan ya bayyana cewa irin wannan mummunar ɗabi’a ta cin zarafi malaman addini na iya lalata zamantakewa da tubalin zaman lafiya a tsakanin al’umma.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin yayin tattaunawarsa da malaman addini da na gargajiya a birnin Kaduna, inda ya jaddada muhimmancin rawar da shugabannin addini ke takawa wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai.

Tinubu ya bai wa ’yan wasan ƙwallon kwandon mata kyautar Dala dubu 100 da gidaje Gwamnatin Kano ta karɓi rahoton binciken Kwamishinan da ya yi belin Danwawu

“Ina nanata cewa, idan muka bari shugabannin addini suka zama abin zagi da cin mutunci ba gaira ba dalili, to ita kanta ƙasar nan za ta lalace balle wata jiha. Duk lokacin da abubuwa suka rikice, wurinsu muke komawa domin neman addu’o’i,” in ji Gwamnan.

Malam Uba Sani ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu ’yan siyasa ke haɗa kai da wasu da ya bayyana da “marasa sanin abin da ya dace” wajen ɓata suna da yi wa malamai ƙage a kafafen sada zumunta.

Ya buƙaci shugabanni da mabiyansu da su guji yin amfani da malaman addini wajen biyan buƙatun siyasa ko na ƙashin kai, yana mai jaddada cewa hakan yana barazana ga zaman lafiya da jituwa da ake morewa a Kaduna da ma ƙasar baki ɗaya.

Gwamnan ya kuma yaba da rawar da malaman addini suka taka tun daga lokacin da ya hau mulki har kawo yanzu, yana cewa sun kasance ginshiƙi wajen samar da zaman lafiya a jihar.

“Da ba don su ba, da babu damar da muke da ita yau ta cin moriyar zaman lafiya a Jihar Kaduna,” in ji shi.

Ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda ’yan siyasa ke watsi da malamai bayan samun nasarar zaɓe, sannan su sake waiwayarsu idan zaɓe ya gabato.

“Muna tunawa da su ne wata ɗaya ko biyu kafin zaɓe. Muna zuwa wajen su da maganganu na yaudara da daɗin baki dangane da addini, domin su mara mana baya.”

Uba Sani ya kuma buƙaci a samar da alaƙa ta dindindin da shugabannin addini, ba sai kawai lokacin da zaɓe ya kusanto ba.

“Malamai da shugabannin addini muhimman jiga-jigai ne a tsarin ƙasa, shi ya sa muke ganin lallai muna buƙatar su a koyaushe wajen shiriya, ba sai lokacin zaɓe ba,” in ji shi.

Ya ce tun farkon mulkinsa, ya samu shawarwari masu amfani daga shugabannin addini kan batutuwan zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a jihar.

A ƙarshe, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bai wa shugabannin al’umma muhimmanci a duk wani sha’ani da ya shafi tsaro, yana mai cewa zaman lafiya mai ɗorewa ba zai samu ba sai da amincewar jama’a da haɗin gwiwa.

“Mun bayyana cewa ba za mu tura jami’an tsaro zuwa kowace unguwa ba tare da tuntubar shugabannin yankin ba. Su za su ɗauki nauyi, su tsara, sannan gwamnati ta tallafa musu,” in ji gwamnan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci gaba
  • An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa
  • Mu daina zagin malaman addini idan muna son zaman lafiya — Uba Sani
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Namijin Kokarinsu
  • Wani Dan Siyasa Ya Shirya Addu’o’i Na Musamman Domin Samun Zaman Lafiya A Zamfara
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri
  • Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu
  • Sai an samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu za mu ajiye makamai — Hamas
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
  • Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC