‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
Published: 23rd, June 2025 GMT
Rundunar ‘yansandan jihar Benuwe ta tabbatar da garkuwa da dukkan fasinjojin wata motar bas ta kamfanin Benue Links a hanyar Eke, Ugbokolo a karamar hukumar Okpokwu ta jihar a yammacin Lahadi. Wani ganau da ya zanta da LEADERSHIP ta wayar tarho, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7 na yammacin ranar Lahadi, inda wasu ‘yan bindigar suka tare wata motar bas din da ta taho daga Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, suka yi awon gaba da fasinjojin da ke cikinta bayan sun kwace kayayyakinsu, sannan suka tafi da su cikin daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: jihar Benuwe
এছাড়াও পড়ুন:
Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin da wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a Jihar Kano.
Aminiya ta gano yadda fashewar bam ɗin ya haddasa firgici a yankin da lamarin ya faru, inda jami’an tsaro da na agajin gaggawa suka garzaya wajen don kai ɗauki.
An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000 Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a FilatoKwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke yin jigilar ne wanda aka yi sakaci ya fashe.
“Na samu kiran gaggawa cewa wani abu mai tayar da hankali ya faru. Da na isa wajen, sai na ga abin kamar bama-baman sojoji ne suka fashe.
“Mutane 15 sun jikkata, kuma abin takaici, guda biyar sun rasu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa yankin domin samun kulawa ta gaggawa.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa wata babbar mota ce ɗauke da kayan fashewar, wadda ta ke kan hanyar zuwa Jihar Yobe.
Har yanzu jami’an tsaro ba su tabbatar da ko motar sojoji ce ke ɗauke da kayan fashewar ba.
Rundunar na ci gaba da da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin da kuma abin da ya haddasa fashewar abun.
“Za mu samu cikakken bayani bayan kammala bincike,” in ji Kwamishinan.
Ya kuma roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu.
Ga hotunan yadda jami’an tsaro ke bincike kan lamarin: