Rundunar ‘yansandan jihar Benuwe ta tabbatar da garkuwa da dukkan fasinjojin wata motar bas ta kamfanin Benue Links a hanyar Eke, Ugbokolo a karamar hukumar Okpokwu ta jihar a yammacin Lahadi. Wani ganau da ya zanta da LEADERSHIP ta wayar tarho, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 7 na yammacin ranar Lahadi, inda wasu ‘yan bindigar suka tare wata motar bas din da ta taho daga Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, suka yi awon gaba da fasinjojin da ke cikinta bayan sun kwace kayayyakinsu, sannan suka tafi da su cikin daji.

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Benuwe, Edet Udeme ya bayyana cewa, lamarin ya rutsa ne da wata motar bas kirar Toyota mai lamba 14B-143BN, wadda aka same ta a gefen titi a Ugbokolo, cikin karamar hukumar Okokwu. A cewar Udeme, da samun rahoton lamarin, tawagar ‘yansanda tare da hadin gwiwar sojoji da kuma ‘yan sa kai na al’ummar jihar Benuwe, suka yi gaggawar zuwa wurin. “A lokacin da rundunar ta tsunduma dajin, ta ceto daya daga cikin fasinjojin, mai suna Paul Terns, wanda ya yi nasarar tserewa daga hannun masu garkuwar”. Udeme ta kara da cewa, an tura karin wasu sojoji a yankin domin kara kaimi wajen neman sauran fasinjojin da kuma tabbatar da dawowarsu cikin koshin lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Benuwe

এছাড়াও পড়ুন:

Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin da wasu 15 suka jikkata sakamakon fashewar wani bam a Jihar Kano.

Aminiya ta gano yadda fashewar bam ɗin ya haddasa firgici a yankin da lamarin ya faru, inda jami’an tsaro da na agajin gaggawa suka garzaya wajen don kai ɗauki.

An yi wa ma’aikatan ƙananan hukumomin Gombe ƙarin albashin N5,000 Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato

Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce fashewar na iya kasancewa bam ɗin da sojoji suke yin jigilar ne wanda aka yi sakaci ya fashe.

“Na samu kiran gaggawa cewa wani abu mai tayar da hankali ya faru. Da na isa wajen, sai na ga abin kamar bama-baman sojoji ne suka fashe.

“Mutane 15 sun jikkata, kuma abin takaici, guda biyar sun rasu,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitocin da ke kusa yankin domin samun kulawa ta gaggawa.

Ya ce binciken farko ya nuna cewa wata babbar mota ce ɗauke da kayan fashewar, wadda ta ke kan hanyar zuwa Jihar Yobe.

Har yanzu jami’an tsaro ba su tabbatar da ko motar sojoji ce ke ɗauke da kayan fashewar ba.

Rundunar na ci gaba da da bincike domin gano musabbabin faruwar lamarin da kuma abin da ya haddasa fashewar abun.

“Za mu samu cikakken bayani bayan kammala bincike,” in ji Kwamishinan.

Ya kuma roƙi jama’a da su kwantar da hankalinsu.

 

Ga hotunan yadda jami’an tsaro ke bincike kan lamarin:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • ’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 
  • Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato
  • An kashe uban ango da ɗan uwansa a harin Filato
  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata