Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar da fara atisayen sojan ruwa na hadin gwiwa da kasashen Rasha da Iran, wanda za a ci gaba da gudanarwa har zuwa mako mai zuwa a kusa da tashar ruwa ta Chabahar  ta kasar Iran.

Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar a yau Lahadi cewa, kasashen Sin, Rasha da Iran sun fara atisayen jiragen ruwa na hadin gwiwa daga tashar ruwan Chabahar ta Iran ne domin karfafa hadin gwiwa na tsaro tsakanin wadannan kasashe guda uku.

Kwanaki biyu da suka gabata, Beijing ta mayar da martani ga kalaman sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth na cewa kasarsa a shirye take domin shiga kowane irin yaki, kuma idan muna son dakile Sinawa ko wasu, dole ne mu kara karfinmu na yaki, inji sakataren tsron na Amurka.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya ce, kalaman da jami’in na Amurka ya yi suna haifar da sabani da kuma yada abin kasar Sin ke kallonsa a matsayin barazana ga kasarta.

Lin ya kara da cewa, “Muna kira ga Amurka da ta daina gina tunaninta  akan masaniyarta dangane da Sin a lokutan baya, musamman lokacin yakin cacar baki, domin kuwa a yanzu Sin ba wadda Amurka ta san ice a lokutan baya ba.

Sakataren tsaron Amurka ya fada a wata hira da kafar yada labarai ta Fox News a ranar Larabar da ta gabata cewa, Amurka ta shirya tsaf domin shiga kowane irin yaki a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar dokokin Gombe ta fara duba ƙudirin ƙirƙirar sabbin gundumomi 13

Majalisar Dokokin Jihar Gombe, ta fara duba ƙudirin ƙirƙirar sabbin gundumomin ci gaban Ƙananan Hukumomi 13 da Gwamna Inuwa Yahaya ya gabatar.

Ƙudirin ya tsallake karatu na farko da na biyu cikin rana guda.

Zaɓen cike gurbi: An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a Zariya An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano

Kakakin majalisar, Abubakar Muhammad Luggerewo, ya bayyana hakan ne yayin zaman sauraron ra’ayin jama’a a kan ƙudirin, wanda aka gabatar wa majalisar kwanaki uku da suka gabata.

Ya ce majalisar ta yi gaggawar karanta ƙudirin saboda muhimmancinsa, domin zai taimaka wajen kusantar da gwamnati ga jama’a.

Hakazalika ya ce zai kawo ci gaba a ƙauyuka, da kuma tabbatar da amfani da dukiyar jihar ta hanyar da ta dace.

Kakakin ya ƙara da cewa an shirya sauraron ra’ayin jama’a domin samun shawarwari daga al’umma, shugabanni da ƙungiyoyi domin ƙara wa ƙudirin armashi.

Taron ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar dokokin Gombe ta fara duba ƙudirin ƙirƙirar sabbin gundumomi 13
  • Aragchi: Yiyuwan Sake Shiga Yaki Da HKI Nan Kusa Yana Da Wuya
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • China Tace Bata Goyon Bayan A Sake Dorawa Iran Takunkuman MDD
  • India Ta Dage Kan Maida martani da hana Shigowar Kayakin Amurka Kasar
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Iran Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ya Bayyana Isra’ila A Matsayar ‘Yar Yaudara