Iran, Rasha da China, sun fara wani atisayin sojojin ruwa a kusa da tashar ruwa ta Chabahar
Published: 9th, March 2025 GMT
Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar da fara atisayen sojan ruwa na hadin gwiwa da kasashen Rasha da Iran, wanda za a ci gaba da gudanarwa har zuwa mako mai zuwa a kusa da tashar ruwa ta Chabahar ta kasar Iran.
Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar a yau Lahadi cewa, kasashen Sin, Rasha da Iran sun fara atisayen jiragen ruwa na hadin gwiwa daga tashar ruwan Chabahar ta Iran ne domin karfafa hadin gwiwa na tsaro tsakanin wadannan kasashe guda uku.
Kwanaki biyu da suka gabata, Beijing ta mayar da martani ga kalaman sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth na cewa kasarsa a shirye take domin shiga kowane irin yaki, kuma idan muna son dakile Sinawa ko wasu, dole ne mu kara karfinmu na yaki, inji sakataren tsron na Amurka.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya ce, kalaman da jami’in na Amurka ya yi suna haifar da sabani da kuma yada abin kasar Sin ke kallonsa a matsayin barazana ga kasarta.
Lin ya kara da cewa, “Muna kira ga Amurka da ta daina gina tunaninta akan masaniyarta dangane da Sin a lokutan baya, musamman lokacin yakin cacar baki, domin kuwa a yanzu Sin ba wadda Amurka ta san ice a lokutan baya ba.
Sakataren tsaron Amurka ya fada a wata hira da kafar yada labarai ta Fox News a ranar Larabar da ta gabata cewa, Amurka ta shirya tsaf domin shiga kowane irin yaki a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman
“An zabo Abubakar Dantsoho ne, daga cikin sauran wadanda aka karamma da lambar yabon bisa kokarin da yake ci gaba da yi, na bunkasa fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar wanda hakan ya sanya, aka kara samun fitar da kaya daga kasar nan, ta hanyar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa dIMODantsohoa tsarin NSW ta hanyar yin amfani da dabarar PCS domin janyo ra’ayin masu zuba jari daga ketare a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, da aka samar da kayan aiki na zamani, ” Inji sanarwar.
“Akawi kuma batun kara daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar a tsakanin hukumomin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma wato PMAWCA da kuma zabar Dantsoho, a matsayin mataimakin shugaban kungiyar masu tafiyar da hukumomin Jiragen Ruwa na kasa da kasa wato IAPH,” A cewar sanarwar.
Hukumar ta NPA ta bayyana cewa, a karkashin shugabancin Dantsoho tare da taimakawar ministan bunkasa tattalin arziki na teku Adegboyega Oyetola, an sake zabar Nijeriya, zuwa mataki na C a karkashin kungiyar kasa da kasa ta tafiyar da harkar sufurin Jiragen Ruwa wato IMO.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA