Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
Published: 21st, June 2025 GMT
Najeriya ta tura sojojinta 197 domin zuwa aikin tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a kasar Gambia.
Dakarun na Najeriya waɗanda tuni suka kammala samun horo, za sai yi aikin wanzar da zaman lafiya a Gambia be a ƙarƙashin rundunar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) da sunan (ECOMIG).
Shugaban Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Uwem Bassey, ya buƙaci sojojin da su kasance masu nuna nuna ƙwarewa da jarumta a yayin gudanar da ayyukansu a ƙasar Gambia.
Ya yi wannan kira ne a jawabinsa a wurin bikin yaye sojojin a Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna, kafin tafiyarsu.
Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar AmurkaManjo-Janar Bassey ya buƙaci sojojin da su guji nuna son kai, su mutunta hakkokin ɗan Adam da kuma dokoki da al’adun al’ummar Gambia.
Ya gargaɗe su game da cin zarafi musamman na jinsi, tare da cewa duk sojan aka samu da laifi zai gamu da tsauraran matakan ladabtarwa.
Bassey ya bayyana cewa Najeriya tana da dogon tarihi na bayar da gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na ƙasar da ƙasa, inda sojojinta ke samun karɓuwa a duniya saboda jaruntakarsu, da ƙwarewarsu.
Sojojin Najeriya sun taka muhimmiyar rawa wajen dawo da zaman lafiya a rikice-rikicen da aka samu a faɗin Afirka da ma duniya, ciki har da Lebanon da Yugoslavia da Laberiya, Saliyo, da Sudan, inda suka ci gaba da samun yabo saboda jaruntakarsu da ƙwarewarsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Najeriya Sojojin Najeriya wanzar da zaman lafiya Zaman lafiya da zaman lafiya a
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Raba Takin Zamani Ga Manoma A Katsina
Rundunar Brigade ta 17 na Sojojin Najeriya da ke Katsina ta raba buhunan takin zamani ga manoma a ƙauyuka shida da ke kusa da sansanin Natsinta, cikin Jibia da Katsina.
Kwamandan brigade ɗin, Birgediya Janar Babatunde Omopariola, ya ce an yi hakan ne don ƙarfafa dangantakar sojoji da al’umma, tare da taimaka musu wajen noma, lafiya da ilimi.
Ya kuma nemi haɗin kan jama’a wajen bayar da bayanai da sintiri domin tabbatar da tsaro a jihar.
A madadin al’umma, shugaban ƙauyen Katoge, Malam Abubakar Bala, ya gode wa sojojin, inda ya bayyana cewa takin zai taimaka wajen bunkasa noma, kuma sun dade suna amfana da tsaro da taimakon sojoji a yankin.
Kauyukan da suka amfana da rabon takin sun hada da Natsinta, Katoge, Garke, Dan-negaba, Unguwar Sarkin Aiki, da Tsangaya.
Daga Isma’il Adamu