Aminiya:
2025-06-21@14:04:45 GMT

Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia

Published: 21st, June 2025 GMT

Najeriya ta tura sojojinta 197 domin zuwa aikin tabbatar da tsaro da wanzar da zaman lafiya a kasar Gambia.

Dakarun na Najeriya waɗanda tuni suka kammala samun horo, za sai yi aikin wanzar da zaman lafiya a Gambia be a ƙarƙashin rundunar Ƙungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) da sunan (ECOMIG).

Shugaban Ayyuka na Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya, Manjo-Janar Uwem Bassey, ya buƙaci sojojin da su kasance masu nuna nuna ƙwarewa da jarumta a yayin gudanar da ayyukansu a ƙasar Gambia.

Ya yi wannan kira ne a jawabinsa a wurin bikin yaye sojojin a Barikin Sojoji na Jaji da ke Jihar Kaduna, kafin tafiyarsu.

Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka

Manjo-Janar Bassey ya buƙaci sojojin da su guji nuna son kai, su mutunta hakkokin ɗan Adam da kuma dokoki da al’adun al’ummar Gambia.

Ya gargaɗe su game da cin zarafi musamman na jinsi, tare da cewa duk sojan aka samu da laifi zai gamu da tsauraran matakan ladabtarwa.

Bassey ya bayyana cewa Najeriya tana da dogon tarihi na bayar da gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na ƙasar da ƙasa, inda sojojinta ke samun karɓuwa a duniya saboda jaruntakarsu, da ƙwarewarsu.

Sojojin Najeriya sun taka muhimmiyar rawa wajen dawo da zaman lafiya a rikice-rikicen da aka samu a faɗin Afirka da ma duniya, ciki har da Lebanon da Yugoslavia da Laberiya, Saliyo, da Sudan, inda suka ci gaba da samun yabo saboda jaruntakarsu da ƙwarewarsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Sojojin Najeriya wanzar da zaman lafiya Zaman lafiya da zaman lafiya a

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe

Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara asibiti da ke Makurdi, Babban Birnin Jihar Benuwe, domin duba waɗanda da suka jikkata a hare-haren da ‘yan bindiga suka jihar.

Shugaban ya je ne domin ganin irin ɓarnar da aka yi, tare da nuna alhini da goyonnsa baya ga al’ummar jihar.

Hare-haren Benuwe: Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a asibiti  Mun shirya yin sulhu da ’yan bindiga — Gwamnatin Sakkwato

Hotunan ziyayar sun nuna Tinubu yana duba da waɗanda abin ya shafa.

Go hotunan a ƙasa:

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
  • Xi Ya Tattauna Da Shugaban Rasha Ta Wayar Tarho
  • Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Tafkin Chadi
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe