Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
Published: 20th, June 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta kama wani mutum mai suna Alexander Peter bisa zarginsa da kashe mahaifiyarsa mai suna Madam Atiny Peter mai shekara 71 da adda.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam a Jihar Akwa Ibom.
Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiyaKwamishinan ’yan sandan jihar, CP Baba Mohammed Azare ne ya tabbatar da kamen a yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, a hedikwatar ’yan sanda da ke Ikot Akpan Abia, a Uyo.
Kwamishinan ’yan sandan ya bayyana cewa, an kama wanda ake zargin Alexander ne a ranar 10 ga watan Yuni, kuma a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin wannan ɗanyen aikin.
“Mummunan lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam, inda rahotanni suka ce wanda ake zargin ya yi amfani da adda ne wajen yi wa mahaifiyarsa kisan gillar,” in ji Kwamishinan, inda ya ce rundunar ’yan sandan na ƙoƙarin bankaɗo lamarin tare da gano musabbabin wannan aika-aika.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, an kama mutane 54 da ake zargi a faɗin jihar a cikin makonni shidan da suka gabata bisa aikata laifuka daban-daban.
Bugu da ƙari, rundunar ta ƙwato makamai da alburusai sama da 50 a wannan lokacin.
Kisan ya haifar da damuwa a cikin al’ummar yankin, inda mazauna yankin suka kaɗu matuƙa game da kisan da ɗan tsohuwar ya yi wa mahaifiyarsa da hannunsa.
‘Yan sanda sun ce za a samu ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Akwa Ibom Kashe mahaifiyarsa
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe ’yan ta’addan IPOB da yawa a Imo — ’Yan Sanda
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Imo, ta ce jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan sanda, sojoji da DSS sun kashe ’yan ta’addan ƙungiyar IPOB da yawa.
Kakakin rundunar, DSP Henry Okoye, ya ce tawagar ta lalata sansanonin IPOB a yankin Ezioha da ke Ƙaramar Hukumar Mbaitoli, da kuma a Umuele, Ubuakpu, da Amakor a Ƙaramar Hukumar Njaba.
’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m NAJERIYA A YAU: Wadanne Kalubale Gwamna Fubara Zai Fuskanta Bayan Dawowa Mulkin Ribas?Ya ce da yawa daga cikin mambobin ƙungiyar sun mutu yayin samamen, wasu kuma an kama su, yayin da wasu suka tsere da raunuka.
Okoye, ya ƙara da cewa an gano bindigogi da harsasai da dama a sansanonin, haka kuma ƙwararru sun lalata abubuwan fashewa da aka samu wuraren.
Rundunar ta jadadda ƙudirinta na wanzar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa tare da roƙon jama’a su yi aiki tare da jami’an tsaro.