Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom
Published: 20th, June 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Akwa Ibom ta kama wani mutum mai suna Alexander Peter bisa zarginsa da kashe mahaifiyarsa mai suna Madam Atiny Peter mai shekara 71 da adda.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam a Jihar Akwa Ibom.
Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiyaKwamishinan ’yan sandan jihar, CP Baba Mohammed Azare ne ya tabbatar da kamen a yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis, a hedikwatar ’yan sanda da ke Ikot Akpan Abia, a Uyo.
Kwamishinan ’yan sandan ya bayyana cewa, an kama wanda ake zargin Alexander ne a ranar 10 ga watan Yuni, kuma a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin wannan ɗanyen aikin.
“Mummunan lamarin ya faru ne a ƙauyen Ikot Inyang da ke ƙaramar hukumar Oruk Anam, inda rahotanni suka ce wanda ake zargin ya yi amfani da adda ne wajen yi wa mahaifiyarsa kisan gillar,” in ji Kwamishinan, inda ya ce rundunar ’yan sandan na ƙoƙarin bankaɗo lamarin tare da gano musabbabin wannan aika-aika.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, an kama mutane 54 da ake zargi a faɗin jihar a cikin makonni shidan da suka gabata bisa aikata laifuka daban-daban.
Bugu da ƙari, rundunar ta ƙwato makamai da alburusai sama da 50 a wannan lokacin.
Kisan ya haifar da damuwa a cikin al’ummar yankin, inda mazauna yankin suka kaɗu matuƙa game da kisan da ɗan tsohuwar ya yi wa mahaifiyarsa da hannunsa.
‘Yan sanda sun ce za a samu ƙarin bayani yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Akwa Ibom Kashe mahaifiyarsa
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta daure mutumin da yake yada bidiyon tsiraici shekara 76 a kurkuku
Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta yanke wa wani mai suna Olukoye Olalekan hukuncin daurin shekaru 76 a kukuku saboda yada hotunan tsiraicin yara kanana da kuma aikata damfara.
Alkalin kotun, Mai Shari’a Alexander Owoeye, ne ya yanke hukuncin ranar Alhamis, bayan ya samu mutumin da aikata laifukan da aka zarge shi da su.
Rikicin Filato: An sake kashe mutum 17 a Mangu da Bokkos 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’An dai gurfanar da Olukoye ne a gaban kotun ana zarginsa da laifuka 18 da suke da alaka da yada hotunan tsiraicin yara kanana, damfara ta intanet, boye kudaden haram da kuma mallakar kadarori ta haramtacciyar hanya, wanda Hukumar Yaki da Rashawa ta EFCC ta zarge shi da aikatawa.
A cewar lauyar masu kara, Bilkisu Buhari-Bala, laifukan sun saba wa tanade-tanaden sassa na 23(1)(c) da 23(1)(f) na kundin laifukan intanet da kuma sassa na 18(3),16(2)(a),16(3),1(1)(a), da 1(2) na kundin hana almundahanar kudade.
Yayin shari’ar, lauyar ta EFCC ta shaida wa kotun cewa Olukoye ya bude wasu shafukan sada zumunta a dandalin sada zumunta irin su Snapchat da Instagram, wadanda ya rika amfani da su a matsayin mace daga jihar North Carolina ta Amurka.
Lauyar ta ce mutumin ya rika amfani da shafukan wajen damfarar mutane har ta kai ga ya mallaki wani gida, ta hanyar yin barazanar wallafa hotunan tsiraicin yara kanana a shafukan.
Da yake yanke shukunci, Mai Shari’a Alexander ya sami Olukoye da dukkan laifukan sannan ya yanke masa hukuncin jimillar daurin shekara 76 a gidan kaso.