Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta
Published: 23rd, June 2025 GMT
Manyan Hafsoshin Tsaro na ƙasar Iran sun sha alwashin mayar wa Amurka da martani mai tsanani wanda sai ta yi da-na-sanin harin da kai wa Iran.
Rundunar Tsaro ta Iran ta sanar da haka ne bayan wani zama da Babban Kwamandan Sojojin ƙasar, Amir Hatami, ya yi da wasu manyan kwamandojinsa.
Harami ya shaida wa taron tsare-tsaren cewa ya zama tilas Amurka ta girbi abin da ya shuka a Iran a wannan karon.
Ya bayyana cewa ko a baya, Iran ta saba koya wa Amurka darasi a duk lokacin da ta takali Iran.
Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —Masani NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin NajeriyaBabban Hafsan Tsaron Iran, Abdolrahim Mousavi, a cikin wata sanarwa, ya ce, Iran ba za ta taɓa ja da baya ba, duk abin da Amurka za ta yi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iran
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Matsalar tare fasinjoji da kashe su a hanyoyin Najeriya na ƙara tsananta, musamman a yankunan Arewa.
Misali, a shekarun baya an sha tare matafiya a kashe su a hanyar Abuja zuwa Kano. A kwanakin baya ma an kashe wasu matafiya a garin Uromi da ke jihar Edo a hanyar su ta komawa Kano.
Sai na kwanan nan da ya faru a Jihar Filato inda aka kashe wasu matafiya da ke kan hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure.
NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne da nufin gano matakan daƙile afkuwar haka a nan gaba.
Domin sauke shirin, latsa nan