Matsayi ya yi maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
Published: 23rd, June 2025 GMT
Ana zargin wani ɗan shekaru 18 da kashe wani maraya ɗan shekara 10 a yankin Ƙaramar Hukumar Zariya ta Jihar Kaduna.
’Yan sanda sun kama matashin ne kan zargin sa da yi wa ɗan yaron, wanda ɗan baffansa ne, ɗaurin goro tare da azabtar da shi saboda yaron ya ƙi amincewa ya yi lalata da shi.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da ta gabata a unguwar Iyan Juma da ke Karamar Hukumar Zariya.
Mahaifiyar marigayin mai suna Asama’u Mohammed ta shaida wa Aminiya cewa, “Na dawo wajen aikatau kamar yadda na saba yi don na samo abin da zan ba su su ci tare da ’yan uwansa, sai ga yayansa ya shigo a guje ya ce ga Idris can a kwance cikin jini kuma fuskarsa a kumbure, wai sun yi faɗa da wani duk an ji mishi ciwo, nan da nan na yafa hijabi ni da ɗan uwar gidana muka tafi inda yake.”
Aminiya ta garzaya Babban Ofishin ’yan sanda da ke Ƙofar Fada cikin birnin Zariya domin ji daga bakin babban jima’i, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin kuma ya shaida wa wakilinmu, cewa sun tattara bayanai yadda lamarin ya kasance kuma sun tura zuwa babban ofishinsu da ke Kaduna
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kaduna DSP Mansur Hassan ya tabbatar wa wakilin namu da faruwar lamarin, da kama wanda da ake zargi.
Ya ƙara da cewa bayan sun kammala bincike za su tora zuwa kuto.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Cin zarafin Wakilin NTA ya tada ƙura a Yobe
Cin zarafin da Babban Jami’an tsaro (CSO) na Gwamnan Yobe, CSP Yakubu Zakari Deba ya yi ga wakilin Talabijin NTA da ke Damaturu, Babagana Kolo a harabar Majalisar Dokokin Yobe da ke Damaturu a ranar Alhamis ya tada ƙura.
Lamarin ya faru ne yayin da wasu ’yan jarida ke jiran a shigar da su cikin zauren domin su bayar da rahoto kan gabatar da kasafin kuɗin 2026 da Gwamna Mai Mala Buni ya yi a gaban Majalisar Dokokin.
An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8 Ƙungiyyar Ƙwallon yashi ta Kada BSC ta fatattaki Kebbi BSCShaidu sun ce Babban Jami’in tsaro (CSO) na fadar gwamnatin Yobe, CSP Yakubu Zakari Deba, ya afka wa Kolo ya buge shi a fuska, lamarin da ya yi sanadiyyar raunuka a bakinsa da wasu ɓangarorin jikinsa.
An ruwaito cewa, lamarin ya kawo cikas ga yadda kafofin yaɗa labarai ke yaɗa labaran taron yayin da ‘yan jarida ke barazanar ƙauracewa gabatar da kasafin kuɗin.
Sai da Kwamishinan Yaɗa labarai, Alhaji Abdullahi Bego ya sa baki kafin ‘yan jaridar su ci gaba da ayyukansu.