Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
Published: 25th, June 2025 GMT
Gwamnatin Nijeriya ta ce babu wata barazanar tsaro a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.
Nijeriya ta musanta batun yiwuwar kai hari kan ’yan Amurka da suke zaune a kasar, sakamakon rikicin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.
Gwamnatin ta bayyana haka ne a matsayin martani dangane da gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ’yan ƙasarta da ke birnin Abuja.
A sanarwar da Ministan Watsa Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar, ya ce, “Gwamnatin Nijeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ’yan ƙasarta da ke Abuja game da tsaro.
“Duk da Gwamnatin Nijeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci — ciki har da na Amurka — ke da shi na ba ’yan ƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Nijeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”
Sanarwar ta ƙara da cewa babu dalilin wannan gargaɗi saboda akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya Gwamnatin Nijeriya barazanar tsaro Nijeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
Yanzu haka ana shirye-shiryen gudanar da taron kasa da kasa na tattauna batutuwan raya tattalin arziki na Davos na yanayin zafi karo na 16, taron da aka fi sani da dandalin Davos. A bana za a gudanar da taron ne tsakanin ranakun Talata 24 zuwa Alhamis 26 ga watan nan na Yuni, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin, bisa taken “sana’o’i a sabon zamani.”
A bana taron zai mayar da hankali ne ga muhimman fannoni biyar, wadanda suka hada da warware batu game da tattalin arzikin duniya, da hange game da kasar Sin, da halin da masana’antun duniya suka fuskanta na taka musu birki, da zuba jari kan al’umma da duniyar bil’adama da batun sabbin makamashi da hajoji.
Game da hakan, jami’i a hukumar tsara manufofin ci gaba da aiwatar da sauye-sauye ta kasar Sin Chen Shuai, ya ce Sin za ta yi amfani da taron na Davos na bana, wajen jaddada aniyarta, ta ci gaba da kwazo don cimma nasarar bude kofa bisa matsayin koli, da rarraba damammakinta na ci gaba da ta samu tare da sauran sassan kasa da kasa.
A nata bangare kuwa, Gim Huay Neo, babbar daraktar dandalin tattalin arziki na duniya, ta shaidawa wani taron menema labarai da ya gudana a baya bayan nan cewa, daya daga cikin yankunan duniya mafiya samun sauye-sauye a duniya shi ne nahiyar Asiya, nahiyar da ke kunshe da kaso 60 bisa dari na ci gaban tattalin arzikin duniya, kuma cikin wannan adadi kasar Sin ita kadai na bayar da gudummawar rabin kason ci gaban nahiyar. Jami’ar ta kara da cewa, dandalin Davos na bana zai samar da zarafi ga mahalartansa, na zurfafa fahimtarsu ga salon ci gaban Sin da sauran sassan Asiya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp