Aminiya:
2025-09-24@15:48:24 GMT

Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja

Published: 25th, June 2025 GMT

Gwamnatin Nijeriya ta ce babu wata barazanar tsaro a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.

Nijeriya ta musanta batun yiwuwar kai hari kan ’yan Amurka da suke zaune a kasar, sakamakon rikicin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta

Gwamnatin ta bayyana haka ne a matsayin martani dangane da gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ’yan ƙasarta da ke birnin Abuja.

A sanarwar da Ministan Watsa Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar, ya ce, “Gwamnatin Nijeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ’yan ƙasarta da ke Abuja game da tsaro.

“Duk da Gwamnatin Nijeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci — ciki har da na Amurka — ke da shi na ba ’yan ƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Nijeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”

Sanarwar ta ƙara da cewa babu dalilin wannan gargaɗi saboda akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya Gwamnatin Nijeriya barazanar tsaro Nijeriya ta

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Gyaran Hanya Ne Ya Haddasa Hatsarin Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna – NSIB

A lokacin hatsarin karfen sauya hanyar ya karye gaba daya, wanda ya haifar da hatsarin.

Hukumar ta kuma gano cewa duk da cewa direbobin jirgin ƙwararru ne, ba a ba su sabon horo ba.

An kuma gano cewa wasu muhimman kayan aiki kamar na’urar CCTV, na’urar sadarwa da agogo sun samu matsala.

NSIB ta shawarci NRC da ta gyara dukkanin kayan da suka lalace, ta sanya sabbin karafan sauya hanya, sannan ta riƙa horar da ma’aikata akai-akai don gujewa irin wannan matsala.

A lokacin hatsarin, mutane 21 ne suka ji rauni daga cikin fasinjoji 618 da ke cikin jirgin, amma babu wanda ya rasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Sakkwato Ta Dakatar da Karɓar Kuɗin Makaranta
  • Rashin Gyaran Hanya Ne Ya Haddasa Hatsarin Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna – NSIB
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya
  • Dakarun IRGC: Iran Za Ta Tarwatsa Makiya Tare Da Mayar Da Martani Kan Duk Wani Zalunci
  • Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja