Aminiya:
2025-06-24@19:44:14 GMT

Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO

Published: 24th, June 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce sama da mutane 40 ciki har da ma’aikatan kiwon lafiya aka kashe a harin da aka kai wani asibiti da ke Sudan a ƙarshen mako.

Ofishin hukumar ta WHO da ke Sudan, ya ce daga cikin waɗanda suka mutu akwai ƙananan yara shida da jami’an kiwon lafiya biyar, sannan kuma an yi wa ginin asibitin mummunar ɓarna.

EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn Yarjejeniyar tsagaita wutar Isra’ila da Iran ta samu tasgaro

RFI ya ruwaito cewa an dai kai harin ne kan Asibitin Al Mujlad da ke a yammacin Kordofan a ranar asabar da ta gabata, kusa da inda ake fafatawa tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF, a yaƙin da suke yi tun a watan Afrilun shekarar 2023.

Shugaban WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya nemi a dakatar da kai wa cibiyoyin kiwon lafiya hari, duk da cewa bai ambaci sunan ɓangaren da ake zargi da kai wannan hari ba.

Sai dai ƙungiyoyin kare hakkin ɗan adam sun zargi wani jigin yaƙin sojojin Sudan marar matuƙi da kai wannan hari, da wata sanarwa da aka fitar a ƙarshen mako ta ce mutunen da suka mutu sun kai 9.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
  • Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana
  • ‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’
  • Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano
  • Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi
  • An kashe matar aure, manomi ya jikkata a wani sabon hari a Kaduna
  • Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani