Leadership News Hausa:
2025-11-08@18:30:56 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

Published: 25th, June 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

A cewar sanarwar, a ranar 22 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 10:40 na dare, wasu mutane huɗu ɗauke da bindigu sun kai farmaki gidan Alhaji Dauda, inda suka yi harbe-harbe sannan suka sace shi suka tafi da shi zuwa wani waje da ba a sani ba.

Nan da nan jami’an ‘yansanda, sojoji, ‘yan banga da masu farauta suka haɗa tawaga domin shiga daji don ceto mutumin.

Washegari da safe, ranar 23 ga watan Yuni, da misalin ƙarfe 7 na safe, tawagar ta haɗu da masu garkuwar a ƙauyen Korori.

Sai da aka yi musayar wuta, inda aka kashe ɗaya daga cikinsu, aka ƙwato bindiga ƙirar AK-47 mai harsashi 13.

Sauran kuwa suka tsere cikin daji, kuma ana ci gaba da nemansu.

Abin takaici, ɗan banga Haruna Tasusuno ya samu rauni sakamakon harbi, inda aka garzaya da shi asibiti kuma aka tabbatar da rasuwarsa daga baya.

An samu Alhaji Dauda kwance a daji cikin jini da raunukan sara da adda a jikinsa, kuma likita ya tabbatar da cewa ya rasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ɗan banga Ɗan Kasuwa Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa

Wata kotu a Ƙasar Jamus ta yanke wa wani ma’aikacin jinya hukuncin ɗaurin rai da rai bayan ta same shi da laifin kashe marasa lafiya 10 da kuma yunƙurin kashe ƙarin wasu 27 ta hanyar yi musu allurar guba.

Kotun da ke birnin Aachen a yammacin Jamus, ta tabbatar da cewa mutumin mai shekaru 44 ya aikata laifukan ne tsakanin watan Disamban 2023 zuwa Mayun 2024 a asibitin Wuerselen.

Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia

Kotun ta bayyana cewa laifin da ya aikata babban laifi ne, wanda zai hana shi samun ’yanci bayan shekaru 15 kamar yadda ake yadda a irin waɗannan shari’o’in.

Ba a bayyana sunan mutumin ba, amma masu gabatar da ƙara sun ce yana “wasa da rayuwar marasa lafiyar” da yake kula da su.

Lauyansa ya roƙi kotu ta wanke shi lokacin da aka fara shari’ar a watan Maris.

Masu gabatar da ƙara sun ce mutumin yana yi wa marasa lafiya, waɗanda mafi yawansu tsofaffi ne, allurar magunguna masu sa barci da rage zafi don rage wahalar aikinsa a lokacin dare.

Sun kuma bayyana cewa mutumin yana da matsalar halayya, ba ya nuna tausayawa ga marasa lafiya, kuma bai nuna nadama ba a lokacin shari’ar.

Haka kuma, sun ce yana amfani da morphine da midazolam, wani magani da ake amfani da shi a wasu lokuta wajen aiwatar da hukuncin kisa a Amurka.

An kuma sake zarginsa da yin aiki ba tare da bin ƙa’ida ba, da kuma rashin nuna ƙwazo a aikinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawa
  • Babban Matsalar Jin Kai A Falasdinu, Inda Falasdinawa Miliyan 1.5 Suke Cikin Halin Musiba Da Bala’i
  • Kwalara ta kashe mutum 10 a Ƙaramar Hukumar Adamawa
  • Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa