Aminiya:
2025-06-24@21:15:38 GMT

Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta

Published: 24th, June 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya soki Isra’ila da Iran, bayan zargin ƙasashen biyu da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka ƙulla.

Lamarin na zuwa ne bayan ɓullar rahoton kai wa juna hari daga dukkan ƙasashen biyu, duk da ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ’yan sa’o’in da suka gabata.

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya

Trump ya ce ƙasashen sun daɗe suna faɗa da juna, kuma a wannan mataki ana iya cewa ba su ma san abin da suke yi ba.

Ya ce: “Ba abin da muke so ke nan ba, ina tabbatar muku cewa ina fushi da abin da suka aikata.”

Shugaba Trump ne mutum na farko da ya fara sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ilan da Iran, bayan shafe kwana 12 suna kai wa juna hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila yarjejeniyar tsagaita wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani

Akwai yiwuwar ƙasar Koriya ta Arewa mai ƙarfin makaman nukiliya za ta taimaka wajen gyara tashoshin nukiliyan Iran da hare-haren Amurka suka lalata da kuma gina sababbin masana’antun ƙera makamai masu linzami masu gudun walƙilya a Iran.

Wani masani mai suna Ankit Panda daga cibiyar zaman lafiya ta kasa da kasa ta da ke Amurka, ne ya bayyana hakan, baya Amurka ta kai hare-hare kan tashoshin nukiliya na ƙasar Iran.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito Ankit Panda, yana bayyana cewa matakin zai kawo ƙarshen irin takura da ƙasashen Yamma ke yi wa Iran.

Hakan na zuwa ne bayan da Ma’aikatar Harkokin Wajen Koriya ta Arewa ta yi tir da harin da Amurka ta kai a matsayin keta hurumin ’yanci da kuma tsaron ƙasar Iran.

NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano

Hakan na zuwa ne bayan da Ma’aikatar Harkokin Wajen Koriya ta Arewa ta yi tir da harin da Amurka ta kai a matsayin keta hurumin ’yanci da kuma tsaron ƙasar Iran.

Ta bayyana cewa, “Amurka da Isra’ila su ne kanwa uwar gani a rikici a yankin Gabas ta Tsakiya, sakamakon yake-yake da ƙoƙarin Isra’ila na faɗaɗa girman ƙasarta, tare sa smaun goyon bayan ƙasashen Yamma.

“Ya kamata al’ummomin duniya masu goyon bayan adalci su fito da murya ɗaya aula’anci wannan abin da Amurka da Isra’ila ke yi, kuma su taka musu burki,” in ji sanarwar da kamfanin dillancin labarai na Koriya ta Arewa (KCNA) ya ruwaito.

Ƙawancen soji tsakanin Iran da Koriya ta Arewa ta jima, kuma ana zargin ta taimaka musu wajen haɗawa da musayar makamai masu linzami masu gudun walƙilya masu cin dogon zango.

Ankit ya ce ba lallai ne Koriya ta Arewa ta taimaka wa Iran wurin ginawa ko hanzarta ƙera makaman nukiliya ba, domin gudun kada makaman su je Amurka. Idan hakan ya faru, Amurka na iya gano lagon fasahar makaman Koriya ta Arewar.

Amma dai akwai yiwuwar Koriya ta Arewar za ta iya, lura da yadda ke da ƙwarewa wajen fasahar makamai da kuma yadda a baya da yawaita taimako ta wannan bangare ga Rasha, wata babbar ƙawar Iran.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Mun amince da tsagaita wuta da Iran —Isra’ila
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
  • Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha
  • Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran