Leadership News Hausa:
2025-09-24@11:19:52 GMT

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

Published: 22nd, June 2025 GMT

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya zabi dan wasan tsakiya Bernardo Silba a matsayin sabon kyaftin din kungiyar, jaridar Daily Mail ta rawaito Guardiola ya yanke hukuncin da kan sa inda ya ki ya nemi shawarar sauran yan wasan kungiyar, Silba ya maye gurbin Kebin De Bruyne bayan dan kasar Belgium din ya bar Etihad a karshen kwantiraginsa.

Guardiola ya kuma nada mataimakan kyaftin guda uku kafin fara gasar kakar wasa ta gaba da suka Ruben Dias, Rodri da Erling Haaland, Silba wanda kwantiraginsa zai kare a bazara mai zuwa, ka iya daura kambun kyaftin na Manchester City na kakar wasa daya kawai idan bai samu karin kwantiragi a kungiyar ba.

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Duk da cewa har yanzu bai rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya da City ba, Silba ya ki amincewa da tayin da dama na barin kungiyar a kasuwar musayar yan wasa na baya-bayan nan, kungiyoyin Saudiyya da dama na zawarcin dan wasan na Portugal, sai kuma tsohuwar kungiyarsa ta Benfica da itama ke fatan dawowarsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ranar Zaman Lafiya ta Duniya: Kungiyar Arewa Ta Nemi Ƙarfafa Sirrin Tsaro Don Kare ‘Yan Najeriya

A yayin da ake gudanar da shagulgulan ranar zaman lafiya ta Duniya ta Bana, Kungiyar rajin tabbatar da zaman lafiya da hadin Kai da kuma cigaban Arewacin Nigeria ta yi Kira ga Gwamnati a dukkan matakai da kuma Hukumomin tsaro su karfafa amfani da bayanan tsaro na sirri wajen kare rayukan al’ummar Kasa.

Shugaban Kungiyar ta ACI Dakta Abdullahi Idris ya yi wannan Kira a wani taron manema labarai da Kungiyar ta Kira a Kaduna.

Ya yi bayanin, Kungiyar ta lura da matakan da Gwamnati da Hukumomin tsaro suka dauka domin maido da zaman lafiya a wasu sassan Arewcin Kasar nan.

Dakta Abdullahi Idris ya ce, matakan da aka dauka abin a yaba ne, Amma kuma sun yi kadan matuka wajen magance matsalalon tsaro da suka addabi Kasar nan.

Ya jadda da bukatar ganin Shugabanni da masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro su daina nuna son zuciya da siyasantar da sha’anin tsaron Kasa domin amfanin al’umma.

Dakta Abdullahi Idris ya tunatar da Shugabanni cewa Allah zai tambaye su yadda suka Shugabanci al’umma, a ranar gobe kimyama.

Daga nan sai Shugaban Kungiyar ya bukaci Gwamnati a dukkan matakai da Hukumomin tsaro su rubunya kokarin da suke yi kana su yi amfani da rahitannin tsaro na sirri wajen maganin wannan matsala ta tsaro.

COV/LERE

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarihi da rayuwar Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh (1943-2025)
  • An Kama Tsohon Ɗan Wasan Super Eagles, Victor Ezeji, Kan Zargin Aikata Zambar ₦39.8m
  • Kotu ta hana NUPENG rufe Matatar Ɗangote
  • Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
  • Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025?
  • Ballon d’Or: ’Yan wasa 5 da ke iya lashe kyautar 2025 
  • Korea Ta Arewa Ta Sanar Da Kera Wani  Sabon Makami Na Sirri
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen: ‘Yan Koren Amurka Da Isra’ila Suke Neman Wargaza Hadin Kan Larabawa Da Na Musulmi                         
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci
  • Ranar Zaman Lafiya ta Duniya: Kungiyar Arewa Ta Nemi Ƙarfafa Sirrin Tsaro Don Kare ‘Yan Najeriya