Hukumar kididdigar makamashi ta Amurka US Energy Information Administration (EIA) ta kiyasta cewa a farkon shekarar 2023 an yi dakon kusan ganga miliyan 20 na fetur a a kullum ta tekun.

Wannan ke nufin ana kasuwancin kusan dala biliyan 600 na makamashi duk shekara ta tekun.

Duk wani tsaiko a tekun zai iya jawo matsala a hada-hadar man fetur a duniya, wanda nan take za a iya gani ta hanyar tashin farashin man.

Sai dai masana suna gargadin cewa daukar wannan matakin zai iya zafafa rikicin na Isra’ila da Iran.

Wannan kuwa shi ne zai jawo wasu kasashen cikin rikicin, ciki har da Amurka, wadda take ta’allaka da man fetur daga kasashen Larabawa.

Yaya girman mashigar Hormuz?

Mashigar Hormuz na tsakanin Iran da Oman ne. Tekun na da fadin kilomita 50.

Taswirar tekun ta nuna bangarorin da suke da kyau a tsaya, da wuraren da ba a so a tsaya da kuma tudun mun tsira a tsakanin bangarorin biyu.

Idan tankokin mai za su wuce, sai su wuce ta kusa da tsibirin Greater da Lesser Tunb – inda ake takun-saka tsakanin Iran da kasashen Larabawa kan mallakinsa.

Masana sun ce yaki na cikin abubuwan da suke jawo tsaiko a hada-hada ta mashigar kamar yadda ya faru a yakin Iran da Iran a shekarar 1980 zuwa 1988.

Amfani da tekun domin kare kai?

Masana sun ce a wajen Iran, datse hada-hada a mashigar Hormuz na nufin amfani da wata dama domin kare kanta.

Kamar yadda kasashen duniya suka dade suna adawa da yunkurin Iran na samun nukiliya, manyan kasashen duniya sun sha nanata cewa ba za su bari Iran ta yi amfani da tekun ba wajen shake duniya game da samun makamashi.

Masana sun yi hasashen cewa Iran za ta iya datse mashigar na wani dan lokaci. Amma wasu na ganin Amurka da kawayenta ba za ta bari hakan ya dauki lokaci ba, inda suke hasashen Amurka za ta iya amfani da karfin soji wajen bude mashigar.

Ta yaya Iran za ta iya datse mashigar Hormuz?

A wani bincike da cibiyar bincike ta Congressional Research Serbice ta Amurka ta nuna, ta ce Iran za ta iya daukar matakin a hankali. Hanyoyin sun kunshi:

Sanar da hana sufurin jiragen ruwa ba tare da bayyana hukuncin saba dokar ba

Sanar da tantance jiragen dakon man ko kuma kwacewa

Yin barin wuta kan jiragen dakon

Kai farmaki kan wasu jiragen dakon

Binne wasu nakiyoyin ruwa a tekun

Kai farmaki kan wasu jiragen kasuwanci da na soji

A yakin Iran da Irak, Iran ta yi amfani da makamin Silkworm domin kai farmaki kan tankokin man fetur, sannan ta dasa nakiyoyi a cikin teku.

Daya daga cikin nakiyoyin ne ya fasa jirgin USS Samuel B Roberts, wanda ya sa Amurka ta mayar da martani.

Sai dai duk da haka Iran ba ta datse mashigar ba baki daya, amma ta kara harajin shige da fice, sannan taa lafta wasu ka’idoji da suka jawo cunkuson jirage wajen ficewa daga gabar tekun.

Ƙarfin sojin Iran

Kwana biyu kafin harin Isra’ila da ya kashe kwamandan dakarun juyin juya-halin Iran Manjo Janar Hossein Salami, kwamandan ya ziyarci sashen sojin ruwa da ke aiki a mashigar.

Ya bayyana yankin tekun a matsayin daya daga cikin muhimman yankunan kare kai da kasar ke da su.

Ya bayyana jirgin da zai iya tafiya tsawon kilomita 10 cikin minti uku a yankin.

Janar Salami ya ce za su yi amfani da manyan makaman masu cin dogon zango domin kare kasarsu. Ya kuma ce za su yi amfani da nakiyoyin ruwa.

Salami ya ce za su fadada ayyukan jirage maras matuka.

Me masana suke hasashe?

Masana suna hasashen daya daga cikin hanyoyin da Iran za ta bi domin datse dakon kusan jirage 3,000 da suke wucewa ta tekun a kusan duk wata ita ce dasa nakiyoyi da amfani da jirage masu cin dogon zango domin kai farmaki kan jiragen.

Sojojin Iran da dakarun juyin juya-hali na kasar za su iya kai farmaki kan jiragen dakon man kasashen waje.

Sai dai kuma Amurka da Isra’ila za su iya kai farmaki kan manyan jiragen ruwan soji idan Isra’ila suka yi amfani da su.

Yanzu haka kafar bibiya harkokin tekun kasar da ke amfani tauraron dan’adam sun nuna jiragen yakin Iran a yankin kudancin kasar.

Wadanne kasashe ne za su fi shiga cikin tasku?

Binciken da masana daga cibiyar Borteda suka yi ya nuna cewa Saudiyya tana fitar da danyen mai kusan ganga miliyan 6 a kullum ta Hormuz – sama da duk wata kasa a yankin.

China da India da Japan da Koriya ta Kudu na cikin manyan kasashen da sufurin danyen man fetur ta tekun.

EIA ta kiyasta cewa a 2022, kusan kashi 82 na danyen man fetur da ake dakonsa ta mashigar, kasashen Asia ake zuwa da su.

A ranar 16 ga watan Afrilun 2025, kwana uku kafin Isra’ila ta kai hari kan tsaron sararin samaniyar Iran, kamfanin dillancin labaran Iran IRNA ya ruwaito shugaban Afirka ta Kudu Yoon Suk-yeol ya ce kashi 60 na man fetur din kasar na biyowa ne ta mashigar Hormuz.

Haka kuma EIA ta ce Amurka na shigo da kusan ganga 700,000 na danyen mai ta mashigar a kullum – kimanin kashi 11 na man da take shigo da shi, kuma kashi uku da man da take amfani da shi a kasar.

kasashen turai baki daya ba sa shigo da fetur da ya haura sama da ganga miliyan 1 a kullum.

Don haka, kasashen Larabawa da Asia ne za su fi fuskantar kalubale idan aka datse mashigar, sama da Amurka da turai da suke da alakar siyasa da Isra’ila.

Sannan akwai kasashen Asia da dama da suke da alaka mai kyau da Iran.

Rawar da China za ta taka

China na cikin kasashen da suka fi amfani da man fetur da ake jigila ta Hormuz. Iran na sayar da mai a farashi mai rahusa, kasa da farashin kasuwannin duniya, wanda hakan ya sa kasar ke samun sauki kan takunkumin tattalin arziki da Amurka ta kakaba mata.

Saboda yadda take matukar amfani da man fetur, China ba za ta yi maraba da duk wani abu da zai jawo tashin farashin mai ba, ko kuma samun tsaiko a dakonsa. Wannan ya sa China za ta yi amfani da diflomasiyya wajen hana yiwuwar daukar wannan matakin.

Akwai wata hanya daban bayan tekun?

Saboda barazanar da ake yawan fuskanta ta datse mashigar a shekarun da suka gabata ne ya sa kasashen da suke dakon man fetur a yankin suka samar da wata hanyar daban.

Wani rahoton EIA ya ce Saudiyya ta fara amfani da bututun gabas maso yammaci mai nisan kilomita 1,200, wanda za a iya tura ganga miliyan 5 a kullum.

A shekarar 2019, Saudiyya ta gyara wasu bututun gas domin su yi daukar danyen man fetur.

Hadaddiyar Daular Larabawa ta hada gabar tekunta na tudu da gabar Fujairah da ke gabar Oma da bututun da zai iya daukar gangan mai miliyan 1.5.

A watan Yulin 2021, Iran ta kaddamar da bututun Greh-Jask, wanda zai iya jigilar mai zuwa gabar Oman. Yanzu haka bututun zai iya daukar ganga 350,000 a kullum.

Rahoton EIA ta kiyasta cewa wadannan hanyoyin za su iya jigilar ganga miliyan 3.5 a kullum – kusan kashi 15 na man da ake jigila ta tekun a kullum.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila mashigar Hormuz kai farmaki kan datse mashigar ganga miliyan jiragen dakon ta mashigar

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila

Iran ta lalata cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, wato cibiyar kimiyya ta Weizmann Institute of Science da ke birnin Tel Aviv.

Cibiyar, wadda ke da alaƙa da binciken harkokin sojin Isra’ila, ta sanar da cewa harin da Iran ta kawo ɗin ya yi sanadiyar ɓarnar da ta kai kimanin Dala miliyan 500.

Makaman Iran sun lalata gine-gine da dama a cibiyar, lamarin da ya sanya masu bincike faɗi-tashi don ceto samfurin bincike a cikin ɓaraguzan gini, a yayin da gobarar ke ci.

Wani makami mai linzami ya tarwatsa wani gini mai ɗauke da ɗakunan gwaje-gwaje na zamani da dama, a yayin harin na ramuwar gayya, bayan da Isra’ila ta kashe masana kimiyyar nukiliya na Iran.

Makamin ya faɗo kan cibiyar ne kafin wayewar garin ranar Lahadi, amma babu wanda ya ji rauni domin cibiyar ba kowa a cikinta a lokacin.

Fira Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya ziyarci wurin, inda ya ce, “wannan harin ne dalilin da ya sa Isra’ila ba za a taɓa barin Iran ta mallaki makaman nukiliya ba.”

Idan ba a manta ba, Isra’ila ce ta fara kai hari kan Iran a ranar 13 ga Yuni, bisa hujjar cewa abokiyar gabar tata tana dab da ƙera makaman nukiliya.

Iran, wadda ta dage cewa shirin nukiliyarta don dalilai na zaman lafiya ne kawai, ta mayar da martani da hare-haren makamai masu linzami da na jirage marasa matuƙa a kan Isra’ila.

Hare-haren Isra’ila sun yi sanadiyar mutuwar wasu manyan masana kimiyyar nukiliya na Iran, da manyan shugabannin sojojin Iran, da fararen hula tare da lalata gidaje da tashoshin nukiliya da ababen more rayuwa.

Duk da cewa yawancin binciken cibiyar Weizmann sun danganci fannin gas magunguna da ilimin kimiyya ne, amma tana kuma da alaka da tsaro.

A watan Oktoba na 2024, ta sanar da haɗin gwiwa da babban kamfanin tsaro na Isra’ila, Elbit, kan “kayayyakin da aka samo daga halittu don aikace-aikacen tsaro.”

Cibiyar binciken kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ila, tana da ƙungiyoyin bincike 286, masana kimiyya ma’aikata 191, da daruruwan dalibai.

Iran ta sanar a ranar Juma’a cewa ba za ta tattauna makomar shirin nukiliyarta ba yayin da take fama da hare-hare daga Isra’ila.

Duk ƙoƙarin ƙasashen Turai na jan hankalin Tehran zuwa tattaunawa bai nuna alamun nasara ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta gamu da fushinmu kan shigar wa Isra’ila yaƙinta da Iran — Houthi
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
  • Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi daraja a Isra’ila
  • Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)
  • Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya
  • Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila