A yammacin ranar Alhamis da ta gabata ce sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka aukawa Falasdinawa masu ibada bayan sun gudanar da sallar tarawihi a masallacin Al-aqsa, inda suka kore su daga masallacin da karfi, tare da hana su yin I’itikafi a cikin masallacin.

Da yake tsokaci a cibiyar yada labaran Falasdinu, Ziad Abhais, mai bincike kan al’amuran birnin Kudus, ya jaddada cewa, matakin da gwamnatin sahyoniyawa ta dauka na hana masu ibadar I’itikafi a cikin masallacin Al-Aqsa wani mataki ne na cin zarafi da kuma muzgunawa hakkokinsu na addini.

Ya kara da cewa: Sojojin yahudawan sahyoniya suna amfani da hakan ne don shimfida ikonsu a kan masallacin Al-Aqsa, domin kuwa a shekara ta 2015 an ba da izinin yin I’itikafi a cikin wannan masallaci a duk ranakun watan Ramadan.

Hukumar bayar da agaji ta Musulunci a birnin Kudus ta sanar da cewa sama da masu ibada dubu 80 ne suka gudanar da sallar isha’i da tarawihi a harabar masallacin Al-Aqsa mai albarka a yammacin ranar Alhamis, wadanda akasarinsu mazauna birnin Kudus ne da yankunan da yahudawa suka mamaye a shekara ta 1948.

A daidai lokacin da watan Ramadan ya shiga, sojojin Isra’ila sun jibge dakaru masu yawa a birnin Kudus da kuma kewayen masallacin Al-Aqsa don hana Falasdinawa masu ibada shiga masallacin .

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza

Kamfanin dillancin labarun “Reutres” ya bayyana cewa; Cibiyar da take tafiyar da ayyukan agaji a Gaza, wacce Amurka ta kafa ta, ta bayar da wata shawarar da take cewa; a kafa wa mutanen Gaza hemomi na wucin gadi da za su zama masomin yin hijirarsu zuwa wani wuri daban, a cikin yankin ko a wejensa.

Rahoton kamfanin dillancin labarun na Reuters ya ambato wata majiya mai karfi tana cewa; An gabatarwa da shugaban kasar Amurka shawarar tilastawa mutanen Gaza yin hijira, kuma a cikin kwanakin nan an tatauna wannan batu a fadar mulkin Amurka ta “White House.”

Har ila yau rahoton ya kunshi cewa,tun daga watan Febrairu cibiyar ta fara kokarin tara kudaden da za su kai dalar Amurka biliyan 1 domin aiwatar da Shirin hijirar mutanen Gaza a cikin yankin ko kuma zuwa wajensa, da kuma kwace makaman da suke a hannun ‘yan gwagwarmaya.

A karkashin wannan Shirin da akwai matakai guda uku; Na farko shi ne bayar da kayan agaji. Na biyu shi ne gina hemomi na tsugunar da Falasdinawa a cikinsu. Na uku shi ne fitar da mutanen Gaza zuwa hijira ta dole, wacce babu dadowa.

 A fili yake cewa a cikin matakin farko da har yanzu ake cikinsa, wurin da aka kira na raba kayan agaji, ba komai ba ne,sai tarko na kashe Faladinawa. Duk wanda ya je domin ya karbi kayan agaji, to ya zama abin farautar ‘yan sahayoniya.

Masu kula da wadannan cibiyoyin na agaji da aka kafa kuwa su ne; HKI da wata rundunar sojojin ‘yan ina da yaki ta Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Kenya: Zanga-zanga Ta Tsayar Da Kai Komo A Birnin Nairobi
  • Miliyoyin Yan Najeriya Ne Suka Gudanar da Tattakin Ashoora Wasu Kuma A Makarantunsu…
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato
  • Miliyoyin Mutane Sun Yi Juyayin Imam Husain ( a.s) A Karbala
  • Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa