EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Published: 21st, June 2025 GMT
Bayan karar, lauyan masu shigar da kara, Abdulhamid L. Tukur, ya kira Nnadikwu Izuchukwu Collins, wani jami’in binciken EFCC, domin ya gabatar da gaskiyar lamarin.
Collins ya shaida wa kotun cewa wasu gungun masu zuba jari sun mika koke ga hukumar EFCC a ranar 21 ga Oktoba, 2022, kan FARM360 da MCBHADMOS Trans-Atlantic Trade Limited, bisa zargin cewa kamfanonin sun yaudare su wajen saka hannun jari a harkar noma da kasuwanci tare da “alkwarin mayar da hannun jari.
Ya bayyana cewa kungiyar ta hada baki ta zuba jarin Naira miliyan 93 tare da kamfanonin.
“A yayin gudanar da bincike, an aika da wasikun ayyukan bincike zuwa Hukumar Kula da Canje-canje (SEC), Bankuna, Babban Bankin Nijeriya (CBN), da Hukumar Kula da Harkokin Kasuwanci (CAC), bi da bi,” in ji Collins.
Ya kara da cewa, “An samu martani daga cibiyoyin da ke sama kuma an yi nazari kan hakan.
“Martanin da SEC da CBN suka bayar ya nuna cewa wadanda ake kara, FARM360 da MCBHADMOS Trans-Atlantic Trade Limited, ba su da lasisin yin huldar zuba jari da kasuwanci a Nijeriya.”
Collins ya kuma shaida wa kotun cewa bayanai daga bankin Fidelity sun nuna cewa Naira miliyan 80 da aka karba daga hannun masu zuba jari an yi amfani da su ne don wasu dalilai na kashin kai, ba don hada-hadar zuba jari kamar yadda ya yi alkawari ba.
Ya ce duk daraktocin kamfanonin sun buya, kuma hukumar EFCC na kokarin gano su tare da kama su.
Daga nan ne EFCC ta gabatar da wasu takardu a matsayin shaida a gaban kotu.
Wadannan suka hada da bayanin banki daga bankin Fidelity, takardar koke daga masu zuba jari, da wasikun da aka yi musayarsu da SEC, CBN, da CAC.
Mai shari’a Dipeolu ya karbi takardun kuma ya sanya su a matsayin bayanan hukuma a shari’ar.
An dage sauraron karar har zuwa ranar 8 ga Yuli, 2025, don ci gaba da shari’ar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da babban shirin dashen bishiyoyi miliyan biyar a shekarar 2025.
An fara dashen ne yankin Yanbawa da ke Ƙaramar Hukumar Makoda.
Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin GudiGwamnan ya ce wannan shiri na nufin yaƙi da sauyin yanayi, farfaɗo da ƙasar da ta lalace, da kuma kare muhalli.
Ya ce an fara dashen bishiyoyin a wannan fili tun shekarar 1972, amma aka bari ya lalace.
Yanzu gwamnatinsa ta gyara shi don ya taimaka wajen shawo kan matsalolin fari da sauyin yanayi.
Ya ƙara da cewa wannan shiri yana daga cikin ayyukan muhalli da gwamnatinsa ta aiwatar cikin shekara guda.
Ayyukan sun haɗa da gyaran gonakin dasa itatuwa a Garun Malam da Garko, waɗanda yanzu suke samar da dubban ƙananan itatuwa da ake rabawa a Kananan Hukumomin 44 na jihar.
Ya ce tuni aka farfaɗo da sama da hekta 200,000 na ƙasa da ta lalace.
Hakazalika, ya ce an samar da wata gona mai hekta 100 domin koya wa manoma dabarun noman itatuwa da kayan gona.
Gwamnan, ya bayyana cewa suna haɗin gwiwa da Ƙungiyar Abinci da Aikin Gona ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO), don koyar da yadda ake amfani da ƙasa yadda ya kamata da kula da muhalli.
Ya ce sun kuma fara shirye-shiryen ilmantar da makarantu da al’umma game da sauyin yanayi da muhimmancin kula da muhalli.
Don ɗorewar wannan shiri, gwamnan ya ce an kafa dokar sauyin yanayi da tsarin aiki a Jihar Kano, wanda ya sanya mata hannu.
Haka kuma an kafa ɗakin gwajin gurɓacewar iska da ruwa a Jami’ar Northwest don binciken muhalli.
Ya ce yanzu haka suna fitar da rahotannin lafiyar iska da ruwa a kowane mako daga sabon ɗakin binciken.
Wannan ya nuna cewa gwamnatin tana amfani da kimiyya da bayanai wajen yaƙi da sauyin yanayi.
Gwamnatin ta sake ɗaukar masu tsaron daji, tare da biyansu albashi, sannan ta ɗauki sabbin ma’aikata don kare dazuka a faɗin jihar.
“Dukkanin itacen da muka dasa dole ne ya girma,” in ji gwamnan.
“Shi ya sa muke gina ƙwararrun cibiyoyi da tsarin lura da yadda shirin ke tafiya.”
Za a raba itatuwan a makarantu, wuraren ibada, gonaki, gidaje, wuraren jama’a, da kuma gefen tituna a cikin gari da karkara.
Gwamnan, ya umarci shugabannin Ƙananan Hukumomi 44 su ɗauki shirin da muhimmanci, su tabbatar da gaskiya wajen raba itatuwan.
“Yanzu ne lokacin da ya dace mu dakatar da yaɗuwar hamada, mu yaƙi sauyin yanayi, da hana zaizayar ƙasa.
“Mu daina sare itatuwa ba tare da tunani ba. Kowa ya dasa, ya kula, kuma ya kare itatuwa don kare ƙasarmu da makomar ’ya’yanmu,” in ji shi.
Ya kuma yi kira ga shugabannin gargajiya, matasa, ƙungiyoyi, makarantu da kasuwanni su haɗa kai wajen samar da kyakkyawan muhalli a Kano.
“A yau ne muka ɗauki alhakin gyara ƙasarmu. Allah Ya taimake mu a wannan aikin alheri,” a cewarsa.
Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Muhammad Dahiru Hashim, ya ce wannan shiri na dasa itatuwa ya nuna irin jajircewar Gwamnan wajen kare muhalli.
Ya bayyana cewa shekara guda da ta wuce, suka fara shirin dasa itatuwa miliyan uku.
Wannan sabon shirin ya ƙara faɗaɗa, kuma an yi amfani da itatuwan da aka noma a cikin jihar.
Ya ce an sake farfaɗo da gonakin gwamnati da ke Gwale da Gwarzo, waɗanda yanzu ke samar da itatuwa don ɗorewar wannan shiri.
Ya ƙara da cewa tun da farko Gwamna Abba, ya nuna irin ƙwarewarsa wajen kare muhalli.
Aikin farko da ya halarta bayan ya hau mulki shi ne bikin Ranar Muhalli ta Duniya ta 2023, wanda ya nuna wa jama’a cewa gwamnatinsa na ɗaukar sauyin yanayi da muhimmanci.
“Jihar Kano ba kawai tana dasa itatuwa ba ne. Muna gyara muhalli, muna tsaftace iska, kuma muna dakatar da yaɗuwar hamada.
“Wannan shiri yana nuna sauyi, da kuma makomarmu,” in ji shi.
Ya kuma yaba wa ma’aikatan ma’aikatar muhalli, shugabannin gargajiya, saboda irin goyon bayan da suka bayar don nasarar wannan shiri.