Bayan karar, lauyan masu shigar da kara, Abdulhamid L. Tukur, ya kira Nnadikwu Izuchukwu Collins, wani jami’in binciken EFCC, domin ya gabatar da gaskiyar lamarin.

Collins ya shaida wa kotun cewa wasu gungun masu zuba jari sun mika koke ga hukumar EFCC a ranar 21 ga Oktoba, 2022, kan FARM360 da MCBHADMOS Trans-Atlantic Trade Limited, bisa zargin cewa kamfanonin sun yaudare su wajen saka hannun jari a harkar noma da kasuwanci tare da “alkwarin mayar da hannun jari.

Ya bayyana cewa kungiyar ta hada baki ta zuba jarin Naira miliyan 93 tare da kamfanonin.

“A yayin gudanar da bincike, an aika da wasikun ayyukan bincike zuwa Hukumar Kula da Canje-canje (SEC), Bankuna, Babban Bankin Nijeriya (CBN), da Hukumar Kula da Harkokin Kasuwanci (CAC), bi da bi,” in ji Collins.

Ya kara da cewa, “An samu martani daga cibiyoyin da ke sama kuma an yi nazari kan hakan.

“Martanin da SEC da CBN suka bayar ya nuna cewa wadanda ake kara, FARM360 da MCBHADMOS Trans-Atlantic Trade Limited, ba su da lasisin yin huldar zuba jari da kasuwanci a Nijeriya.”

Collins ya kuma shaida wa kotun cewa bayanai daga bankin Fidelity sun nuna cewa Naira miliyan 80 da aka karba daga hannun masu zuba jari an yi amfani da su ne don wasu dalilai na kashin kai, ba don hada-hadar zuba jari kamar yadda ya yi alkawari ba.

Ya ce duk daraktocin kamfanonin sun buya, kuma hukumar EFCC na kokarin gano su tare da kama su.

Daga nan ne EFCC ta gabatar da wasu takardu a matsayin shaida a gaban kotu.

Wadannan suka hada da bayanin banki daga bankin Fidelity, takardar koke daga masu zuba jari, da wasikun da aka yi musayarsu da SEC, CBN, da CAC.

Mai shari’a Dipeolu ya karbi takardun kuma ya sanya su a matsayin bayanan hukuma a shari’ar.

An dage sauraron karar har zuwa ranar 8 ga Yuli, 2025, don ci gaba da shari’ar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

Alhaji Hassan ya ce duk da matsalolin tsaro da aka samu a kananan hukumomin, Jihar Kaduna ce kan gaba a noman shinkafa a daukacin jihohin da suke Nijeriya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata
  • Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
  • Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya
  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Ba Atiku kaɗai ba ne matsalar PDP — Gwamna Lawal