Mutane 1,018 ne aka kashe a ci gaba da kisan kiyashi kan tsiraru a gabar tekun Syria
Published: 9th, March 2025 GMT
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar da rahoton cewa, adadin fararen hula da aka yi kisan kiyashin na baya-bayan nan daga tsiraru ‘yan Alawite ya kai mutane 1,018 tun daga ranar alhamis zuwa wannan Lahadi.
Kungiyar sa ido ta ce jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria da kuma kungiyoyin da suke kawance da su da suka da alaka da alkaida, sun kashe fararen hula 745 na Alawi a cikin kwanaki uku da suka gabata, wanda ya haura adadin da aka sanar a lokutan baya.
Sai dai Fox News ta buga misali da wata ‘yar Alawiyya, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta bayyana cewa sama da mutane 4,000 ne aka kiyasta an kashe a yankin gabar tekun Syria da kuma cikin ‘yan Alawiyya.
Kungiyar masu tsatsauran ra’ayin ta Hay’at Tahrir al-Sham wadda ke shugabanci a halin yanzu a Syria, wadda kuma it ace tare da taimakon Turkiya da Amurka da wasu kasashen larabawa ta jagoran jagoranci hare-haren da suka kai ga kawo karshen gwamnatin Assad, ta ce za ta kare tsiraru a kasar, a daidai lokacin da ‘yan bindiga da ke karkashin ikonta a halin yanzu suke yi wa fararen hula yankan rago da sunan cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Assad.
Kungiyar sa ido da kare hakkokin dan adam a Syria ta bayar da rahoton ayyukan kisan gilla da dama a cikin ‘yan kwanakin nan, tare da kashe mata da kananan yara.
“Yawancin wadanda aka kashe din an kashe su ne ta hannun wasu da ke da alaka da ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na sabuwar gwamnatin Syria,” in ji rahoton kungiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa
An kashe wani ɗan sanda a wani mummunan hari da ’yan bindiga suka kai gidan Babban Jami’in Ɗan Sanda (DPO) mai kula Babba Ofishin ’Yan Sanda da ke Aujara a Ƙaramar Hukumar Jahun ta a Jihar Jigawa.
Da misalin ƙarfe 4:00 na asuba, ranar 25 ga Nuwamba, 2025, ne wasu ’yan bindiga suka kai farmaki gidan DPO na Babban Ofishin ’Yan Sandan.
Sanarwar rundunar ’yan sanda ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa jami’an tsaro da ke gadin gidan sun yi ƙoƙarin dakile harin, inda aka samu musayar wuta.
A yayin arangamar, biyu daga cikin jami’an sun samu munanan raunuka, aka garzaya da su asibiti domin samun kulawa.
Tinubu ya gana da Janar Christopher Musa bayan Ministan Tsaro ya yi murabus An kama ’yan bindiga 4 a KanoWashegari, ɗaya daga cikin waɗanda suka ji rauni ya rasu a sakamakon tsananin raunukan da ya samu.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Jigawa, Ɗahiru Muhammad, ya yi ta’aziyya ga iyalan mamacin da abokan aikinsa, yana mai tabbatar da cewa rundunar ta fara bincike na musamman domin kamo waɗanda suka aikata wannan ta’addanci.
Bayan harin, rundunar ta ƙara tsaurara matakan tsaro ta hanyar yawaita sintiri da sanya ido a Aujara da maƙwabtan garuruwan domin hana sake faruwar irin wannan barazana.
Kakakin rundunar, SP Shiisu Lawan Adam, ya roƙi al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da ci gaba da ba da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin taimaka wa binciken da ake yi.