Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar da rahoton cewa, adadin fararen hula da aka yi kisan kiyashin na baya-bayan nan daga tsiraru ‘yan Alawite ya kai mutane 1,018 tun daga ranar alhamis zuwa wannan Lahadi.

Kungiyar sa ido ta ce jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria da kuma kungiyoyin da suke kawance da su da suka da alaka da alkaida, sun kashe fararen hula 745 na Alawi a cikin kwanaki uku da suka gabata, wanda ya haura adadin da aka sanar a lokutan baya.

Sai dai Fox News ta buga misali da wata ‘yar Alawiyya, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta bayyana cewa sama da mutane 4,000 ne aka kiyasta an kashe a yankin gabar tekun Syria da kuma cikin ‘yan  Alawiyya.

Kungiyar masu tsatsauran ra’ayin ta Hay’at Tahrir al-Sham wadda ke shugabanci a halin yanzu a Syria, wadda kuma it ace tare da taimakon Turkiya da Amurka da wasu kasashen larabawa ta jagoran jagoranci hare-haren da suka kai ga kawo karshen gwamnatin Assad, ta ce za ta kare tsiraru a kasar, a daidai lokacin da ‘yan bindiga da ke karkashin ikonta a halin yanzu suke yi wa fararen hula yankan rago da sunan cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Assad.

Kungiyar sa ido da kare hakkokin dan adam a Syria ta bayar da rahoton ayyukan kisan gilla da dama a cikin ‘yan kwanakin nan, tare da kashe mata da kananan yara.

“Yawancin wadanda aka kashe din an kashe su ne ta hannun wasu da ke da alaka da ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na sabuwar gwamnatin Syria,” in ji rahoton kungiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa December 13, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing December 13, 2025 Daga Birnin Sin Kakakin Rasha: Kisan Kiyashin Nanjing Ya Nuna Zaluncin Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan December 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa
  • Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin
  • Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing
  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci