Mutane 1,018 ne aka kashe a ci gaba da kisan kiyashi kan tsiraru a gabar tekun Syria
Published: 9th, March 2025 GMT
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar da rahoton cewa, adadin fararen hula da aka yi kisan kiyashin na baya-bayan nan daga tsiraru ‘yan Alawite ya kai mutane 1,018 tun daga ranar alhamis zuwa wannan Lahadi.
Kungiyar sa ido ta ce jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria da kuma kungiyoyin da suke kawance da su da suka da alaka da alkaida, sun kashe fararen hula 745 na Alawi a cikin kwanaki uku da suka gabata, wanda ya haura adadin da aka sanar a lokutan baya.
Sai dai Fox News ta buga misali da wata ‘yar Alawiyya, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta bayyana cewa sama da mutane 4,000 ne aka kiyasta an kashe a yankin gabar tekun Syria da kuma cikin ‘yan Alawiyya.
Kungiyar masu tsatsauran ra’ayin ta Hay’at Tahrir al-Sham wadda ke shugabanci a halin yanzu a Syria, wadda kuma it ace tare da taimakon Turkiya da Amurka da wasu kasashen larabawa ta jagoran jagoranci hare-haren da suka kai ga kawo karshen gwamnatin Assad, ta ce za ta kare tsiraru a kasar, a daidai lokacin da ‘yan bindiga da ke karkashin ikonta a halin yanzu suke yi wa fararen hula yankan rago da sunan cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Assad.
Kungiyar sa ido da kare hakkokin dan adam a Syria ta bayar da rahoton ayyukan kisan gilla da dama a cikin ‘yan kwanakin nan, tare da kashe mata da kananan yara.
“Yawancin wadanda aka kashe din an kashe su ne ta hannun wasu da ke da alaka da ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na sabuwar gwamnatin Syria,” in ji rahoton kungiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
Ana fargabar cewa wata mata mai suna Success ta kashe wata yarinya mai shekaru bakwai, Alicia Olajumoke, a unguwar Rumueme da ke birnin Fatakwal na Jihar Ribas.
Mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa matar da ake zargin tana da kusanci da dangin mahaifiyar yarinyar, wacce ita kaɗai ce a wurin iyayenta.
El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin NijeriyaBayanai sun ce ita ma matar ta caka wa kanta wuƙa a wuya bayan kashe yarinyar, kuma bayan an garzaya da duk su biyun asibiti, likitoci suka tabbatar da cewa sun riga mu gidan gaskiya.
Lamarin wanda ya faru a ranar Talata ya ɗimauta mazauna yankin, la’akari da zargin cewa matar ta kashe yarinyar ce a gidanta bayan ta je har makarantarsu ta ɗauko ta ba tare da izinin mahaifiyarta ba.
Jami’ar hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sanda a Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, inda ta ce an kai gawar yarinyar ɗakin ajiye gawa domin bai wa likitoci damar kammala bincikensu na kimiyya gabanin soma nasu binciken.
“Mun ziyarci wurin da abin ya faru, mun ɗauki hotuna, kuma an garzaya da su asibiti inda aka tabbatar da mutuwarsu.”