Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar da rahoton cewa, adadin fararen hula da aka yi kisan kiyashin na baya-bayan nan daga tsiraru ‘yan Alawite ya kai mutane 1,018 tun daga ranar alhamis zuwa wannan Lahadi.

Kungiyar sa ido ta ce jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria da kuma kungiyoyin da suke kawance da su da suka da alaka da alkaida, sun kashe fararen hula 745 na Alawi a cikin kwanaki uku da suka gabata, wanda ya haura adadin da aka sanar a lokutan baya.

Sai dai Fox News ta buga misali da wata ‘yar Alawiyya, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta bayyana cewa sama da mutane 4,000 ne aka kiyasta an kashe a yankin gabar tekun Syria da kuma cikin ‘yan  Alawiyya.

Kungiyar masu tsatsauran ra’ayin ta Hay’at Tahrir al-Sham wadda ke shugabanci a halin yanzu a Syria, wadda kuma it ace tare da taimakon Turkiya da Amurka da wasu kasashen larabawa ta jagoran jagoranci hare-haren da suka kai ga kawo karshen gwamnatin Assad, ta ce za ta kare tsiraru a kasar, a daidai lokacin da ‘yan bindiga da ke karkashin ikonta a halin yanzu suke yi wa fararen hula yankan rago da sunan cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Assad.

Kungiyar sa ido da kare hakkokin dan adam a Syria ta bayar da rahoton ayyukan kisan gilla da dama a cikin ‘yan kwanakin nan, tare da kashe mata da kananan yara.

“Yawancin wadanda aka kashe din an kashe su ne ta hannun wasu da ke da alaka da ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na sabuwar gwamnatin Syria,” in ji rahoton kungiyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato

A harin, mutane 13 daga cikin baƙin suka rasu, ciki har da mata da yara.

Kakakin ‘yansandan jihar, DSP Alfred Alabo, ya bayyana cewa za a gurfanar da waɗanda ake zargin.

Daga baya kuma, Kwamishinan ‘Yansandan zai yi jawabi a hedikwatar rundunar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 13 A Neja
  • Abdullahi Ojlan Ya Sanar Da Kawo Karshen Fada Da Makami
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato