Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
Published: 24th, June 2025 GMT
Iran ta kama mutane shida kan zargin kasancewa ’yan leken asiri ga Isra’ila.
Rahotannin kafofin watsa labarai na ƙasar Iran sun nuna cewa mutanen shida suna leken asiri ne ga hukumar leken asiri ta Isra’ila, Mossad, kuma an kama su ne a lardin Hamadan da ke yammacin kasar.
Ali Akbar Karimpour, wani jami’in Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran ya bayyana cewa an kama “‘yan cin amanar ƙasar,” ne a garuruwan Hamadan, Razan, da Nahavand a cikin lardin.
Ya kara da cewa ana zargin su da gudanar da ayyukan ta intanet da nufin haifar da tashin hankalin jama’a, ɓata sunan gwamnatin Iran, da kuma gurɓata sunanta.”
Iran ta kama mutane da dama kuma ta kashe wasu da dama saboda leƙen asiri ga Isra’ila tun bayan fara yaƙinta da Isra’ila.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan leƙen asirin Isra ila Iran
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Cutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.
A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu kuwa gani suke yi zaki da maiko ne ke kawo ta.
Wannan shine abun da da yawa daga cikin mutane suka sani kan wannan cuta, sai dai masana kiwon lafiya na da nasu fahimtar daban kan wannan cuta.
NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya DAGA LARABA: Yadda ‘Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar MakamaiShirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan cutar basir da hanyoyin magance ta.
Domin sauke shirin, latsa nan