2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
Published: 20th, June 2025 GMT
Jagororin jam’iyyun adawa na Najeriya a ƙarƙashin ƙungiyar hadaƙa ta Nigeria National Coalition Group (NNCG) na neman yin rajistar All Democratic Alliance (ADA) domin ta zama sabuwar jam’iyyar da za su yi amfani da ita don tunkarar Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.
NNCG ta riga ta miƙa takardar neman rajistar jam’iyya ga Hukumar Zaɓe mai zaman kanta INEC a hukumance don babban zaɓe na gaba.
Takardar wadda suka aika zuwa ga shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu a ranar 19 ga watan Yuni, wanda shugaban ADA na ƙasa Cif Akin Ricketts da sakataren riƙo Abdullahi Musa Elayo ne suka sanya mata hannu, sannan INEC ta karɓa tare a ranar Juma’a 20 ga Yunin.
A takardar an rubuta cewa, “muna neman INEC ta amince da buƙatarmu ta yi wa ƙungiyarmu ta All Democratic Alliance (ADA) ta zama jam’iyyar siyasa.”
Ta ƙara da cewa, taken jam’iyyar dai shi ne ‘Adalci ga kowa’ sannan masara ce tambarinta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar
এছাড়াও পড়ুন:
Wata mata ta ƙona al’aurar ’yarta da wuta kan zargin maita a Bauchi
Wata mata mazauniyar garin Magama Gumau a Ƙaramar Hukumar Toro, Jihar Bauchi, ta shiga hannun ’yan sanda biyo bayan ƙona al’aurar ’yarta mai shekaru 10 kacal a duniya, kan zargin maita.
Rahotanni sun nuna cewa matar ta yi amfani da cokali ta hanyar sanya shi a wuta ya yi zafi sannan ta umarci ’ya’yanta biyu suka riƙe yarinyar sannan ta ƙona ta.
Janye Dokar Ta-ɓaci: Fubara ya koma Ribas ’Yan bindiga sun kai hari sakatariyar ’yan jarida ta jihar YobeWannan ya jefa yarinyar cikin mawuyacin hali, inda ta ke fama wahalar yin fitsari da bayan gida.
Bayan lamarin ya faru, maƙwabta sun kai ƙarar matar wajen ’yan sanda.
An garzaya da yarinyar zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) domin kula da ita.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce an kama matar da wasu, ciki har da wata mai maganin gargajiya mai suna Fatima Abdullahi, wadda ta karɓi kuɗin matar sannan ta tabbatar mata cewa yarinyar mayya ce.
A cewar rundunar, lamarin ya faru ne ranar 11 ga watan Satumba, 2025.
Tuni Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike, tare da tabbatar da adalci.
’Yan sanda sun kuma ja hankalin iyaye da su daina kai yara wajen bokaye, domin hakan na iya jawo ɓarna maimakon samun waraka.