2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
Published: 20th, June 2025 GMT
Jagororin jam’iyyun adawa na Najeriya a ƙarƙashin ƙungiyar hadaƙa ta Nigeria National Coalition Group (NNCG) na neman yin rajistar All Democratic Alliance (ADA) domin ta zama sabuwar jam’iyyar da za su yi amfani da ita don tunkarar Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.
NNCG ta riga ta miƙa takardar neman rajistar jam’iyya ga Hukumar Zaɓe mai zaman kanta INEC a hukumance don babban zaɓe na gaba.
Takardar wadda suka aika zuwa ga shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu a ranar 19 ga watan Yuni, wanda shugaban ADA na ƙasa Cif Akin Ricketts da sakataren riƙo Abdullahi Musa Elayo ne suka sanya mata hannu, sannan INEC ta karɓa tare a ranar Juma’a 20 ga Yunin.
A takardar an rubuta cewa, “muna neman INEC ta amince da buƙatarmu ta yi wa ƙungiyarmu ta All Democratic Alliance (ADA) ta zama jam’iyyar siyasa.”
Ta ƙara da cewa, taken jam’iyyar dai shi ne ‘Adalci ga kowa’ sannan masara ce tambarinta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Alhaji Atiku Abubakar
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗaruruwan Tsaffin Jami’an Tsaron Isra’ila Sun Roki Trump Ya A Dakatar Da Yakin Gaza
Wata tawagar jami’an tsaron Isra’ila da suka yi ritaya su 600 ciki har da tsaffin shugabannin hukumomin leƙen asiri sun aika wa Shugaban Amurka, Donald Trump wasiƙa domin neman ya matsa wa Isra’ila da ta gaggauta kawo ƙarshen yaƙin da ake a Gaza.
Jami’an sun ce “tunaninmu ne cewa Hamas ta daina zama wata barazana ga Isra’ila”.
“Amincin da kake da shi a wajen Isra’ilawa zai ƙara ba ka damar sanya Firaiminista [Benjamin] Netanyahu da gwamnatinsa a kan hanya daidaitacciya: A kawo ƙarshen yaƙin, a dawo da mutanen da ke tsare a kuma daina gallaza wa Falasɗinawa,” kamar yadda suka rubuta.
Roƙon nasu na zuwa ne daidai lokacin da rahotanni ke cewa Netanyahu na ƙoƙarin faɗaɗa ayyukan soji a Gaza yayin da tattaunawar tsagaita wuta da Hamas ke fuskantar cikas.
Isra’ila ta ƙaddamar da mummuman yaƙi a Gaza sakamakon hare-haren Hamas a Kudancin Isra’ila ranar 7 ga Oktoban 2023 inda aka kashe kusan mutum 1,200 sannan aka yi garkuwa da mutum 251 a Gaza.
Fiye da mutum 60,000 aka kashe sakamakon yaƙin da Isra’ila ta ƙaddamar a Gaza tun lokacin, kamar yadda ma’aikatar lafiyar Hamas ta shaida.
‘Ƙawayen Isra’ila sun fara ƙaurace mata’: Ƙasashen duniya sun fara juya wa Netanyahu baya Yadda Birtaniya da ƙasashen duniya 28 suka caccaki Isra’ila kan yaƙin Gaza