Aminiya:
2025-10-17@18:37:10 GMT

EFCC ya kama manyan jami’an NNPC kan badaƙalar Dala 7.2bn

Published: 24th, June 2025 GMT

Hukumar EFCC mai yaki da masu karya tattalin arziki ta tsare wasu tsofafin manyan jami’an Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) kan zargin badakalar kudade da yawansu ya kai Dala biliyan 7.2.

Jami’an EFCC sun tsare tsohon Babban Jami’in Kudi na NNPCL, Umar Ajiya Isah da kuma tsohon Manajan-Daraktan Matatar Mai ta Warri, Jimoh Olasunkanmi, kan zargin almundahanar.

Wani babban jami’in EFCC da ya nemi a boye sunansa ya ce hukumar ta tsare tsoffin manyan jami’an na NNPC ne kan zargin wadaka da kudaden gyaran matatun mai da ke Kaduna da Warri da kuma Fatakwal.

Wakilinmu ya yi kokarin samun karin haske daga kakakin EFCC, Dele Oyewale, amma jami’in bai amsa duk kiraye-kirayen da aka yi masa da kuma rubutattun sakon da aka tura masa domin samun bayani a hukumance.

Umar Ajiya ya kasance mai kula da harkokin kula da kudaden gyaran matatun guda uku da kuma da kuma manyan jami’an da ke aiki.

Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6 Iyalan Kanawa da aka kashe a Uromi sun zargin gwamnati da yin watsi da su

Wani jami’in EFCC ya bayyana cewa hukumar tana kuma bincikar was jami’an NNPC da ke kula da wasu muhimman ayyuka kan zargin su da karkatar da kudade da kuma karbar na-goro daga ’yan kwangila.

A cewarsa, wadanda binciken ya shafa sun hada da Manajan-Daraktan Matatar Warri, Tunde Bakare; tsohon Manajan-Daraktan Matatar Fatakwal, Ahmed Adamu Diko da wani tsohon Manajan-Daraktan matatar, Ibrahim Monday Onoja.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kwangila Matatar mai Manajan Daraktan manyan jami an

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Kula Da GIdajen Gyaran Hali A Zamfara Ta Neman Shigarda Fursunoni Tsarin Inshorar Lafiya Na NHIS

Kwanturola na hukumar gyaran Hali a Najeriya reshen jihar Zamfara, Murtala Muhammad Haruna, ya yi kira da a shigar da fursunoni cikin tsarin inshorar lafiya na kasa (NHIS) domin tabbatar da samun ingantattun ayyukan kiwon lafiya.

 

Ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga kwamishiniyar lafiya ta jihar Zamfara, Dakta Nafisa Muhammad Maradun, a ofishinta da ke Gusau.

 

Haruna ya ce shirin ya yi dai-dai da hangen nesan babban kwamandan hukumar gyaran hali ta Najeriya da nufin inganta jin dadin fursunonin da ke gidajen yari.

 

Kwantirolan ya kuma jaddada bukatar inganta asibitin hukumar da ke cibiyar tsaro ta matsakaita, Gusau, da samar da isassun kayan aikin likita da magunguna masu mahimmanci don biyan bukatun kiwon lafiyar fursunoni.

 

Murtala Mohammed Haruna ya lura da cewa, matakin ya dace da ajandar sabunta bege na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda ya mayar da hankali kan inganta jin dadin daukacin ‘yan Najeriya, ciki har da wadanda ke tsare.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Mustapha Abubakar ya fitar, ya ce sun kai ziyarar ne da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumar gyaran hali da ma’aikatar lafiya ta jihar domin inganta harkokin kiwon lafiya ga fursunonin dake fadin jihar ta Zamfara.

 

Da take mayar da jawabi, Dakta Nafisat Muhammad Maradun ta yabawa hukumar gidan yari bisa jajircewar da take yi na kula da fursunonin da kuma kare lafiyar jama’a.

 

Ta bayyana cewa tuni Gwamna Dauda Lawal ya siyo kayayyakin jinya da kayan aikin da ya yi alkawari a ziyarar da ya kai gidan gyaran hali na Gusau.

 

A cewarta, nan ba da jimawa ba za a mika magungunan da aka sayo ga hukumar, yayin da za a sanya kayan aikin da zarar an kammala inganta asibitin.

 

Kwamishinan ta ba da tabbacin cewa Konturola na ma’aikatar a shirye yake a karkashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal, don yin hadin gwiwa da Hukumar Kula da Lafiya don inganta harkar kiwon lafiya.

 

Ta kara da cewa hadin gwiwar za ta hada da tallafin fasaha don gyare-gyare, inganta kayan aiki, da tsarin shiga NHIS.

 

 

 

REL/AMINU DALHATU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
  • An ceto mutane 3 da aka yi garkuwa da kama wasu a Bauchi
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba
  • Hukumar Kula Da GIdajen Gyaran Hali A Zamfara Ta Neman Shigarda Fursunoni Tsarin Inshorar Lafiya Na NHIS
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Bayyana Cewa: Sake Gina Gaza Zai Ci Dala Biliyan 70
  • Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta