Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto
Published: 9th, March 2025 GMT
A karon farko alkaluman ta’addaci a yankin Sahel da ke nahiyar Afirka ya zarce na jimillar sauran sassan duniya, a cewar rahoton cibiyar GTI mai bincike kan ta’addanci a matakin duniya.
Rahoton ya nuna yawan kashe-kashe masu alaka da ta’addanci a Sahel, “ya zarce rabin jimillar adadin a duniya.”
Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a KanoAlkaluman sun nuna an kashe mutane 3,885 a yankin daga cikin mutane 7,555 da aka kashe a fadin duniya a dalilin ta’addanci.
Rahoto ya kara da cewa a yayin da adadin a matakin duniya ya ragu daga kimanin 11,000 a shekarar 2015, lamarin ya ninku sau 10 a yankin daga shekarar 2019, sakamakon yadda kungiyoyin ta’addaci ke fadada ayyukansu a yankin.
Ya ci gaba da cewa, yayin da ake samun daidaikum masu aikata ta’addanci a kasashen Yammacin Duniya, a yankin Sahel kuma ana samu karuwar kungiyoyi ta’addanci masu mubaya’a ga kungiyar IS da Alka’ida, irin su ISWAP da Boko Haram da sauransu.
Shugaban Cibiyar Binciken Tsaro ta Afirka, Niagalé Bagayoko, ya ce wadannan kuniyoyi, “suna kafa dokoki, a wani lokaci ma har gasa suke yi da juna wajen nuna iko.”
Cibiyar Nazarin Tattalin Arziki da Zaman Lafiya, mai bincike kan zaman lafiya da tashe-tashen hankula a duniya ce ta walla fa rahoton, wanda ya bayyana ta’addanci a matsyain “abin da kungiyoyin da ba gwamnati ba ke yi na barazana ko tursasawa ko tashin hankali domin cim-ma manufar siyasa ko tattalin arziki ko addini da sauransu.”
Yankin Sahel da rahoton ya ayyana dai ya kunshi kasashe 10 — Burkina Faso, Mali, Nijar, Kamaru, Guinea, The Gambia, Senegal, Nijeriya, Chadi da uma Mauritania — kuma a nan ne sulusin mutane ’yan kasa da shekara 25 a fadin duniya suke.
GTI ta bayyana cewa tun bayan juyin mulkin kasar Mali a shekarar 2020 da 201 kungiyar IS-Sahel take ta fadada ikonta a iyakar kasar da Burkina Faso da Nijar, haka ma kungiyar JNIM, inda suke ta daukar karin mayaka, ciki har da kananan yara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Kasashen Duniya yankin Sahel
এছাড়াও পড়ুন:
Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu
Hukumar kare hakkin bil’adama ta “Human Right Watch” ta fitar da wani rahoto da a cikin ta bayyana cewa; kungiyar nan mai ikirarin jihadi a kasar Burkina Faso, ( Jama’at Nusratul-Islam wal Muslimin) da kuma kungiyar Daular Musulunci a cikin yankin Sahara, sun kashe fararen hula 50 daga watan Mayu zuwa yanzu.
Rahoton ya ci gaba da yin bayanin cewa, a cikin Ogusta kungiyoyin na masu riya cewa suna yin jihadi sun kashe mutane 40 a cikin garuruwan Djibo da Youba.
Rahoton ya kuma ce; a watan Yuli kuwa kungiyar IS ta kai wa fararen hula hari da suke kan hanyar kai kayan agaji zuwa garin Gorom-Gorom da aka killace da hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 9.
Kungiyar kare hakkin bil’adama din ta ce, wadannan irin hare-haren sun sabawa dokokin kasa da kasa na jin kai, kuma suna a matsayin laifukan yaki.
Kungiyar kare hakkin bil’adaman ta “Human Right Watch” ta mika sakamakon binciken da ta gabatar ga hukumomin tsaro da na shari’a na kasar ta Burkina Faso. Sai dai har yanzu babu wani martani da ta samu.
Shekaru 3 kenan da kasar ta Burkan Faso take a karkashin mulkin soja da su ka sha alwashin kawo karshen masu tayar da kayar baya da sunan jihadi.
Tun daga 2016 ne kungiyoyin dake dauke da makamai suke kai hare-hare a sassa mabanbanta na kasar ta Burkina Faso da sunan jihadi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci