Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto
Published: 9th, March 2025 GMT
A karon farko alkaluman ta’addaci a yankin Sahel da ke nahiyar Afirka ya zarce na jimillar sauran sassan duniya, a cewar rahoton cibiyar GTI mai bincike kan ta’addanci a matakin duniya.
Rahoton ya nuna yawan kashe-kashe masu alaka da ta’addanci a Sahel, “ya zarce rabin jimillar adadin a duniya.”
Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a KanoAlkaluman sun nuna an kashe mutane 3,885 a yankin daga cikin mutane 7,555 da aka kashe a fadin duniya a dalilin ta’addanci.
Rahoto ya kara da cewa a yayin da adadin a matakin duniya ya ragu daga kimanin 11,000 a shekarar 2015, lamarin ya ninku sau 10 a yankin daga shekarar 2019, sakamakon yadda kungiyoyin ta’addaci ke fadada ayyukansu a yankin.
Ya ci gaba da cewa, yayin da ake samun daidaikum masu aikata ta’addanci a kasashen Yammacin Duniya, a yankin Sahel kuma ana samu karuwar kungiyoyi ta’addanci masu mubaya’a ga kungiyar IS da Alka’ida, irin su ISWAP da Boko Haram da sauransu.
Shugaban Cibiyar Binciken Tsaro ta Afirka, Niagalé Bagayoko, ya ce wadannan kuniyoyi, “suna kafa dokoki, a wani lokaci ma har gasa suke yi da juna wajen nuna iko.”
Cibiyar Nazarin Tattalin Arziki da Zaman Lafiya, mai bincike kan zaman lafiya da tashe-tashen hankula a duniya ce ta walla fa rahoton, wanda ya bayyana ta’addanci a matsyain “abin da kungiyoyin da ba gwamnati ba ke yi na barazana ko tursasawa ko tashin hankali domin cim-ma manufar siyasa ko tattalin arziki ko addini da sauransu.”
Yankin Sahel da rahoton ya ayyana dai ya kunshi kasashe 10 — Burkina Faso, Mali, Nijar, Kamaru, Guinea, The Gambia, Senegal, Nijeriya, Chadi da uma Mauritania — kuma a nan ne sulusin mutane ’yan kasa da shekara 25 a fadin duniya suke.
GTI ta bayyana cewa tun bayan juyin mulkin kasar Mali a shekarar 2020 da 201 kungiyar IS-Sahel take ta fadada ikonta a iyakar kasar da Burkina Faso da Nijar, haka ma kungiyar JNIM, inda suke ta daukar karin mayaka, ciki har da kananan yara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Kasashen Duniya yankin Sahel
এছাড়াও পড়ুন:
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.
Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA