Aminiya:
2025-08-07@08:16:28 GMT

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato

Published: 22nd, June 2025 GMT

An yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a garin Mangu, da ke Ƙaramar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Waɗanda aka kashe sun haɗa da maza, mata da yara.

Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani Mahaifin Rahama Sadau ya rasu

Dukkaninsu mazauna unguwar Basawa-Anguwan Rimi ne da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.

Sun tashi ne daga Zariya zuwa Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan da ke Jihar Filato domin halartar ɗaurin aure, amma aka kai musu hari a hanya.

An yi jana’izarsu tare da birne su da yammacin ranar Asabar a maƙabartar Hayi, ƙarƙashin tsauraran matakan tsaro.

Malamai a Mangu sun ce iyalan mamatan sun amince a birne su a Filato domin kaucewa shiga tashin hankali a garinsu.

Kafin yi musu jana’iza, malamai sun roƙi Musulmai su ɗauki lamarin a matsayin ƙaddara daga Allah, su kuma guji ɗaukar doka a hannunsu.

Sheikh Suleiman Haruna, ɗaya daga cikin malamai a yankin da ya jagoranci jana’izar, ya buƙaci jama’a da su zauna lafiya tare da yin haƙuri da juna.

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya yi Allah-wadai da harin, inda ya umarci jami’an tsaro da su kamo masu hannu a lamarin.

Ga hotunan yadda jana’izar ta wakana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗaurin Aure hari Zariya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu

Majalisar Dokki ta Jihar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu ta jihar, bayan ta yi wa daftarin dokar karatu na daya har zuwa na uku.

A sabuwar dokar da aka yi wa kwaskwarima, wadda take jiran sa hannun Gwamna Umaru Dikko Radda, gwamnan jihar ne kadai ke da ikon daga darajar sarki.

Kazalika ta ba wa gwamnan jihar kadai ikon zabar masu zabar sarki, sa’annan ta kara yawan da masu zaben sarki daga mutane hudu zuwa biyar.

Kauran Katsina, Galadiman Katsina, ’Yandakan Katsina da Durbi su ne mutum hudu da aka sani a mastayin masu zabar sarki, amma yanzu dokar ta da Marusan Katsina Hakimin Shargalle, sarautar da aka ba wa tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika.

Gobara ta cinye gidan hakimi a Bauchi Nafisa ta cancaci kyautar Dala 100,000 da gida da OON —Pantami Ɗaliba ’yar shekara 15 daga Yobe ta lashe Gasar Muhawara ta Duniya

A makon da ya gabata ne masarautar ta ba wa Hadi Siriki wannan sarauta wadda aka dauke ta daga Dutsi, yayin da ita Dutsin kuma aka mayar da Baburtau a matsayin mukamin Hakimin.

Gabanin wannan sabuwar doka a satin da ya gabata ne Masarautar Katsina ta fitar da sunayen wasu hakiman da aka kirkiro a masarautar.

Bayan waccan sanarwa, sai kuma ga kwafin ita wannan doka wadda majalisar ta yi wa karatu na yawo a kafofin sada zumunta.

Kazalika, akwai ’yan Majalisar Masarautun na Katsina da Daura wadanda aka yi wasu canje-canje.

A yanzu ’yan majalisar sun qunshi wakilai biyu da malamai, biyu daga attajiran jihar, wakili daga sashen kungiyoyin matasa. Sauran su ne, wakilin Kwamishinan Kananan Hukumomi, wakili daga Ma’aikatar Masarautu da masu zaben sarki.

Hatta da Sakataren Majalisa za a turo shi ne daga gwamnati maimakon a da sarki ne ke zabar shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya
  • Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
  • Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Jihar Kano Ya Sha Alwashin Kawar Da Badala A Harkokin Fina-finai
  • Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Majalisar Katsina ta amince da sabuwar Dokar Masarautu
  • An Kaddamar Da Shirin Dashen Itatuwan Dabino Miliyan 50 A Jigawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA