Aminiya:
2025-06-23@10:50:31 GMT

Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano

Published: 23rd, June 2025 GMT

Wasu mutum biyu sun rasu a cikin masai a yayin da suke ƙoƙarin ciro wata ƙaramar waya da ta faɗa a ciki shaddar a yankin Ƙaramar Hukumar Albashi ta Jihar Kano.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce mutanen biyu sun gamu da ajalinsu ne a ranar Asabar a unguwar Bazabe da ke ƙaramar hukumar.

Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya sanar cewa a safiyar ranar Asabar ne aka sanar da ofishin kwana-kwana ta samu kiran gaggawa game da lamarin.

Ya bayyana cewa wani ɗan shekara 40 ya shiga masai domin ciro wayarsa da ta faɗa a ciki, amma sai ya maƙale a ciki.

A sakamakon wani mai suna Ibrahim ya shiga domin ciro shi, amma bayan ya yi nasarar sanya masa igiya, sai shi ma ya yanke jiki ya fadi a ciki.

Daga baya hukumar ta yi nasarar fito da su ta kai asibiti inda aka tabbatar cewa sun rasu.

Hukumar ta mika gawarwakinsu ga Babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Ƙaramar Hukumar Albasu domin ci gaba bincike da sauran abubuwan da suka dace.

Daga ƙarshe Hukumar ta buƙaci jama’a da su daina jefa kansu a cikin haɗari su rika neman taimako daga ƙararru a duk lokacin da wani abu na gaggawa ya taso.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: waya

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya

Jagororin jam’iyyun adawa na Najeriya a ƙarƙashin ƙungiyar hadaƙa ta Nigeria National Coalition Group (NNCG) na neman yin rajistar All Democratic Alliance (ADA) domin ta zama sabuwar jam’iyyar da za su yi amfani da ita don tunkarar  Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

NNCG ta riga ta miƙa takardar neman rajistar jam’iyya ga Hukumar Zaɓe mai zaman kanta INEC a hukumance don babban zaɓe na gaba.

Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna Wani ya kashe mahaifiyarsa mai shekara 71 a Akwa Ibom

Takardar wadda suka aika zuwa ga shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu a ranar 19 ga watan Yuni, wanda shugaban ADA na ƙasa Cif Akin Ricketts da sakataren riƙo Abdullahi Musa Elayo ne suka sanya mata hannu, sannan INEC ta karɓa tare a ranar Juma’a 20 ga Yunin.

A takardar an rubuta cewa, “muna neman INEC ta amince da buƙatarmu ta yi wa ƙungiyarmu ta All Democratic Alliance (ADA) ta zama jam’iyyar siyasa.”

Ta ƙara da cewa, taken jam’iyyar dai shi ne ‘Adalci ga kowa’ sannan masara ce tambarinta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano
  • HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar ’yan ɗaurin auren da aka kashe a Filato
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Bom ya kashe mutum 5 a Kano — ’Yan sanda
  • Bam ya kashe mutum 5, 15 sun jikkata a Kano
  • Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
  • An sallami ƙarin ma’aikata 639 a tashar Muryar Amurka
  • 2027: Manyan ’Yan adawa na neman rajistar sabuwar jam’iyya
  • Jami’an tsaro sun ƙwato makamai da kama mutane 398 a Kaduna