Aminiya:
2025-08-07@21:45:17 GMT

Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano

Published: 23rd, June 2025 GMT

Wasu mutum biyu sun rasu a cikin masai a yayin da suke ƙoƙarin ciro wata ƙaramar waya da ta faɗa a ciki shaddar a yankin Ƙaramar Hukumar Albashi ta Jihar Kano.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce mutanen biyu sun gamu da ajalinsu ne a ranar Asabar a unguwar Bazabe da ke ƙaramar hukumar.

Kakakin hukumar, Saminu Yusif Abdullahi, ya sanar cewa a safiyar ranar Asabar ne aka sanar da ofishin kwana-kwana ta samu kiran gaggawa game da lamarin.

Ya bayyana cewa wani ɗan shekara 40 ya shiga masai domin ciro wayarsa da ta faɗa a ciki, amma sai ya maƙale a ciki.

A sakamakon wani mai suna Ibrahim ya shiga domin ciro shi, amma bayan ya yi nasarar sanya masa igiya, sai shi ma ya yanke jiki ya fadi a ciki.

Daga baya hukumar ta yi nasarar fito da su ta kai asibiti inda aka tabbatar cewa sun rasu.

Hukumar ta mika gawarwakinsu ga Babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Ƙaramar Hukumar Albasu domin ci gaba bincike da sauran abubuwan da suka dace.

Daga ƙarshe Hukumar ta buƙaci jama’a da su daina jefa kansu a cikin haɗari su rika neman taimako daga ƙararru a duk lokacin da wani abu na gaggawa ya taso.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: waya

এছাড়াও পড়ুন:

Duk wanda ya haka rijiyar burtsatse a Lekki ruwan masai yake sha – Gwamnatin Legas

Gwamnatin jihar Legas ta yi gargadin cewa akwai yiwuwar duk wanda yake haka rijiyar burtsatse a unguwar masu hannu da shuni ta Lekki da ke jihar, ruwan masai yake sha.

Babban Sakatare a ofishin da ke kula da magudanun ruwa da tsaftar ruwan sha a jihar, Mahmood Adegbite ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan samar da ruwan sha a jihar a kwanakin baya.

DAGA LARABA: Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani? ‘Za a yi ambaliyar kwana 5 a jihohi 19 na Najeriya’

Mahmood ya kuma ce gurbataccen ruwan sha a unguwar zai iya haifar da barazanar lafiya matukar ba a bi hanyoyin da suka dace wajen tsaftace shi ba.

Ya ce, “Game da batun kula da tsaftar muhalli kuwa, zan iya cewa duk wanda ya haka burtsatse a yankin unguwar Lekki, watakila yana shan ruwan da zan iya kira da ruwan masai ne.

“Amma idan muka yi kokari wajen sarrafa dattin da yake fitowa daga yankin kamar yadda muke yunkurin yi a yanzu haka, za mu dakile duk wata cuta da za ta iya yaduwa sanadiyyar rashin tsafta,” in ji shi.

Sai dai ya ce akwai jan aiki a gaban jihar wajen magance matsalar ambaliyar ruwa, yana mai cewa ko a watan da ya gabata sai da aka samu ambaliyar a wasu sassan jihar, sabanin a watan Agustan da aka saba gani a shekarun baya.

“Maganar gaskiya a bangaren ambaliya, duk da muna namijin kokari wajen magance ta, amma har yanzu akwai jan aiki a gabanmu kafin mu iya magance matsalar baki daya,” in ji Babban Sakataren.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato
  • Gwamnatin Kwara Ta Horar Da Manoma Sama Da 500 Tare Da Basu Tallafi
  • An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara
  • ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
  • Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
  • Jami’an Alhazai Sun Karrama DG Labbo Bisa Nasarar Hajjin 2025
  • Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Jihar Kano Ya Sha Alwashin Kawar Da Badala A Harkokin Fina-finai
  • Duk wanda ya haka rijiyar burtsatse a Lekki ruwan masai yake sha – Gwamnatin Legas
  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Ɗaruruwan Tsaffin Jami’an Tsaron Isra’ila Sun Roki Trump Ya A Dakatar Da Yakin Gaza