Aminiya:
2025-08-06@09:18:39 GMT

Za mu ci gaba da yi wa Isra’ila luguden wuta — Shugaban Iran

Published: 22nd, June 2025 GMT

Shugaban Ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta ci gaba da mayar da martani kan hare-haren da Isra’ila ke kai mata.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake magana da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ta wayar tarho.

Uba Sani ya yi jajen ’yan ɗaurin aure 12 da aka kashe a Filato Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno

Shugaba Pezeshkian ya ce Iran tana da niyyar yin haɗin gwiwa da sauran ƙasashe don amfani da makamashin nukiliya ta hanyar da ba ta da alaƙa da yaƙi, amma hakan ba yana nufin za su dakatar da inganta shirye-shiryensu na nukiliya gaba ɗaya ba.

Ya ƙara da cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa ƙasarsa ba za su wuce haka nan ba, domin kuwa Iran za ta riƙa mayar da martani mai zafi.

A ranar Asabar, rundunar sojin Iran ta yi gargaɗi cewa za ta kai wa Isra’ila ta hark ta jiragen ruwa.

A cewar wani kakakin rundunar sojin Iran da ya bayyana a wani bidiyo, duk ƙasar da ta tura makamai zuwa Isra’ila, kamar ta shiga yaƙi da Iran ce kai-tsaye, kuma Iran ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen kare kanta ba.

A ranar Juma’ar da ta gabata, Iran ta harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa zuwa Isra’ila, lamarin da ya jikkata mutane aƙalla 19 a birnin Haifa da ke Arewacin Isra’ila, kamar yadda wani asibiti a yankin ya tabbatar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila Shugaban Ƙasa yaƙi

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri

Babban kwamandan sojojin Iran ya jaddada cewa; Ƙarfin makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa ciki suna nan kuma a shirye suke don aiki

Babban kwamandan sojojin kasar Iran, Manjo Janar Amir Hatami ya bayyana cewa: Karfin makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki na sojojin gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na ci gaba da aiki gadan-gadan, kuma a shirye suke su gudanar da ayyuka,  yana mai cewa: A lokacin yaki na baya-bayan nan suna  ci gaba da kai hare-hare har zuwa lokacin da aka gabata da shirin tsagaita bude wuta kan makiya.

A wata ganawa da ya yi da kwamandoji da jami’an rundunar sojojin kasa, Manjo Janar Hatami ya bayyana cewa: Gwamnatin ‘yan sahayoniyya makiya ce mai taurin kai, kuma a tsawon kwanaki 12 da aka shafe ana gwabzawa, an shaida wasu laifuffuka da ta’addanci da ta  yi kan al’ummar Iran, duk da cewa wannan makiya sananniya ce ga al’ummar Iran, kuma an san tarihin wuce gona da irita na zalunci da barna na tsawon kusan shekaru 80 da suka gabata musamman a Gaza yayin kusan shekaru biyu da suka gabata,

Ya kara da cewa: “Duk da irin hasarar da Iran ta yi, da suka hada da shahadar manyan kwamandojin kasarta, manyan malamai, da kuma ‘yan kasa masu daraja, da taimakon Allah, jajircewar mujahidai da karfin gwiwar al’umma, sun sanya an yi nasara a wannan arangama, tare da janyo mummunar barna ga makiya musamman hana su cimma burinsu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Tana Kokarin Boye Barnarta A Zirin Gaza August 3, 2025 Tsohon Shugaban Amurka Joe Biden Ya Caccaki Trump Kan Rusa Kundin Tsarin Mulkin Kasar August 3, 2025 IRGC Tace Bata Amince Da Kasashen Biyu A Kan Kasar Falasdinu Ba August 3, 2025 Iran Da Japan Suna Iya Jagorantar Duniya Don Rabata Da Makamai Kare Dangi August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa Ba za ta Ajiye Makamanta ba Sai Bayan samar Da Kasar falasdinu August 3, 2025 Kungiyar Hamas Ta Wallafa Hotunan bidiyo Na Fursinan HKI tsare A Gaza August 3, 2025 Sojojin HKI, Daga Jiya Zuwa Yau lahadi Kadai Sun Kashe Falasdinawa 62 August 3, 2025 Pezeskkian Ya Ce: Suna Fatan Musayar Kasuwancin Tsakanin Iran Da Pakistan Ta Haura Dala Biliyan 10 August 2, 2025 Araqchi: Abokantaka Da Ke Tsakanin Iran Da Pakistan Wata babbar Jari Ce Nan Gaba August 2, 2025 Jaridar Isra’ila Ta Ce: Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Sha Kashi A Yakin Gaza   August 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Hadin Kai Tsakanin Cibiyoyi  Na Tabbatar Da Karfi Da Ci gaba
  • Giwa LG: Matar Shugaban Karamar Hukuma Ta Kaddamar da Makon Shayar da Nono
  • Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
  • Baghaei : Ziyarar Pezeshkian a Pakistan ta bude wani sabon Shafin alaka
  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
  • Iran Ta Ce Ba Wani Ma’aikacin Hukumar IAEA A Kasar A Halin Yanzu
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Duba Titi Mai Tsawo Kilomita 49
  • Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Karfin Makamai Masu Linzami Da Jiragen Sama Marasa Matuka Ciki Suna Nan Cikin  Shiri