Aminiya:
2025-06-24@00:38:00 GMT

Leeds ta ɗauki ɗan bayan Udinese Jaka Bijol

Published: 24th, June 2025 GMT

Leeds United ta kammala ɗaukar ɗan wasan bayan ƙungiyar Udinese na ƙasar Slovenia, Jaka Bijol mai shekaru 26 kan farashin fam miliyan 15.

Wannan dai shi ne sabon ɗan wasa na biyu da ƙungiyar ta ɗauka bayan zuwan ɗan wasan gaban Jamus, Lukas Nmecha, kyauta.

‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’ Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka

Cefanen Bijol da Leeds ta yi zai ƙara wa ƙungiyar tagomashi wajen tsaron bayanta a yayin da ake shirye-shiryen dawowa sabuwar kakar wasanni ta Firimiyar Ingila.

Bijol dai ya buga ƙasarsa Slovenia wasanni 63 ciki har da rawar gani da ya taka a gasar Euro 2024, inda suka yi canjaras da Ingila a wasannin cikin rukuni gabanin rashin nasara a hannun Portugal yayin bugun daga kai sai mai tsaron raga daf da tafiya matakin kwata-fainal.

Bijol ya shafe kaka uku a yana taka wa Udinese leda a gasar Serie A, inda ya haska a wasanni 95 bayan dawowarsa ƙungiyar ta Italliya daga CSKA Moscow, inda ya shafe shekaru hudu.

Leeds dai ta samu nasarar haurowa Firimiyar Ingila a watan Mayun da ya gabata, bayan ta karkare gasar Championship ta maki 100 daidai da Burnley wadda ta bai wa rata da kwallaye.

AFP

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Bayan faruwar lamarin ne, wasu fusatattun dalibai matasa suka tare hanyar Agaie-Lapai, suna nuna rashin amincewarsu da kisan da aka yi wa abokin su.

 

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce, “Yau 23 ga watan Yuni, 2025 da misalin karfe 3 na dare, rundunar ta samu labarin cewa, da misalin karfe 2:30 na dare wasu ‘yan daba sun kai hari a wasu dakunan kwanan dalibai dake unguwar Ndakitabu ta Lapai, amma maharan sun tsere a lokacin da jami’an ‘yansandan suka isa wurin”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’
  • CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026
  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
  • Koriya ta Arewa za ta taimaka wa Iran gyara tashoshin nukiliyan da Amurka ta kai hari —Masani
  • Dole a ɗauki mataki kan waɗanda suka kashe ’yan ɗaurin aure a Filato — Uba Sani
  • ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa