Leeds ta ɗauki ɗan bayan Udinese Jaka Bijol
Published: 24th, June 2025 GMT
Leeds United ta kammala ɗaukar ɗan wasan bayan ƙungiyar Udinese na ƙasar Slovenia, Jaka Bijol mai shekaru 26 kan farashin fam miliyan 15.
Wannan dai shi ne sabon ɗan wasa na biyu da ƙungiyar ta ɗauka bayan zuwan ɗan wasan gaban Jamus, Lukas Nmecha, kyauta.
‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’ Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin AmurkaCefanen Bijol da Leeds ta yi zai ƙara wa ƙungiyar tagomashi wajen tsaron bayanta a yayin da ake shirye-shiryen dawowa sabuwar kakar wasanni ta Firimiyar Ingila.
Bijol dai ya buga ƙasarsa Slovenia wasanni 63 ciki har da rawar gani da ya taka a gasar Euro 2024, inda suka yi canjaras da Ingila a wasannin cikin rukuni gabanin rashin nasara a hannun Portugal yayin bugun daga kai sai mai tsaron raga daf da tafiya matakin kwata-fainal.
Bijol ya shafe kaka uku a yana taka wa Udinese leda a gasar Serie A, inda ya haska a wasanni 95 bayan dawowarsa ƙungiyar ta Italliya daga CSKA Moscow, inda ya shafe shekaru hudu.
Leeds dai ta samu nasarar haurowa Firimiyar Ingila a watan Mayun da ya gabata, bayan ta karkare gasar Championship ta maki 100 daidai da Burnley wadda ta bai wa rata da kwallaye.
AFP
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tanzania: An Tuhumi Mutane Da Dama Da Laifin Cin Amanar Kasa Bayan Rikicin Zabe
A yau Juma’a ne dai masu shigar da kara a Tanzania su ka gabatar da tuhumar mutane da dama da zargin cin amanar kasa, saboda rawar da su ka taka a cikin rikicin zaben shugaban kasa.
Mutane 76 ne aka tuhuma da cewa; Sun yi kokarin kawo cikas akan zaben da aka yi a ranar 29 ga watan Oktoba da kuma tsokanar mahukunta a birnin Darussalam.
Baya ga laifin cin amanar kasa,ana kuma tuhumar mutanen da cewa sun kitsa aikata laifuka.
Zaben da aka yi a kasar Tanzani a karshen watan Oktoba, ya bar baya da kura saboda tashe-tashen hankulan da aka samu.
Babbar jam’iyyar adawa ta Chadema ta yi zargin cewa an kashe mutane fiye da 1,000,kuma a halin yanzu mahukuntan suna kokari boye duk wata shaida ta laifukan da su ka aikata ta hanyar binne gawawwaki a asirce.
Wadanda su ka sanya idanu a yadda aka gudanar da zaben sun ce, da akwai rashin gaskiya akan yadda aka gudanar da shi.
Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan wacce ta hau karagar Mulki a 2021 bayan rasuwar magabacinta, ta lashe zaben da kawo 97% kamar yadda mahukuntan kasar su ka sanar.
Manyan ‘yan hamayya a zaben shugaban kasar da su ne Tundu Lissu daga jam’iyyar Chadema, da luhaga Mpina na jam’iyyar ACT-Wazalendo, an hana su shiga zaben da aka gudanar. Tarayyar Afirka ta ce masu sa ido da ta aike sun bayyana mata cewa;zaben bai hau ma’auninta na inganci ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Limamin Juma’ar Tehran: Tsayin Dakan ‘Yan Gwagwarmaya Daga Koyi Ne Da Alkur’ani Mai Girma November 7, 2025 Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan November 7, 2025 Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan November 7, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci