Ya nemi ‘yan jarida da su riƙa amfani da kafafen su wajen haska labarai da ke nuna sauye-sauyen da aka samu a hukumomi, yadda jama’a ke shiga cikin harkokin gwamnati, cigaban ababen more rayuwa da bunƙasar tattalin arziki, a matsayin wani ɓangare na rawar da kafafen ke takawa wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya.

“Yayin da muke bikin shekaru 26 na ci gaba da mulkin dimokiraɗiyya a Nijeriya, dole ne kafafen yaɗa labarai su riƙa yaɗa labaran da ke bayyana nasarorin da dimokiraɗiyyar ƙasar nan ta samu, irin su gyaran hukumomi, gina ababen more rayuwa, shiga jama’a cikin harkokin gwamnati, da kuma cigaban tattalin arziki,” inji shi.

Idris ya ƙara da cewa yayin da kafafen yaɗa labarai suke haska waɗannan nasarori ta hanya mai ma’ana, hakan zai taimaka wajen girmama sadaukarwar da ta haifar da dimokiraɗiyyar Nijeriya tare da ƙarfafa haɗin kan ƙasa da amincewar jama’a da gwamnati.

Ya ƙara da cewa, “Ta yin hakan, kafafen yaɗa labarai suna tabbatar da matsayin su a matsayin ginshiƙi wajen ɗorewa da ƙarfafa tafarkin dimokiraɗiyyar Nijeriya.”

Ya kuma sake tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu tana da cikakken niyyar kare ‘yancin faɗar albarkacin baki da ‘yancin kafafen yaɗa labarai.

“Na sha faɗa a wurare da dama, kuma zan sake faɗa a nan, cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da kare ‘yancin kafafen yaɗa labarai a matsayin ginshiƙi kuma tushen dimokiraɗiyyar Nijeriya.

“Za mu ci gaba da ƙarfafa manufofi da shirye-shiryen da za su ba kafafen damar bunƙasa wajen cika nauyin da ya rataya a wuyan su ga dimokiraɗiyya da al’umma,” inji shi.

Ya kuma taɓo ƙalubalen da ‘yan jarida suke fuskanta a wannan zamani na dijital, ciki har da tasirin Ƙirƙirarrar Basira (AI), yaɗuwar labaran ƙarya da rawar da jaridar jama’a ke takawa.

“Bayyanar Ƙirƙirarrar Basira (generative AI) cikin ‘yan shekarun nan ta ƙara dagula lamarin, inda ake cika mu da hotuna da bidiyo na bogi da yaɗa labaran ƙarya, wanda ya sa aikin jarida na gaskiya ya fi wuya, amma kuma ya fi zama wajibi fiye da da,” inji shi.

Ministan ya bayyana cewa ana nan ana aiki tare da UNESCO domin kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai (MIL) ta musamman a Abuja.

“Shi ya sa muke haɗa gwiwa da UNESCO wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai (MIL) a nan Abuja, wacce za ta zama ta farko irin ta a duniya. Da zarar ta fara aiki, wannan cibiyar za ta zama wani babban tushe wajen inganta aikin jarida na gaskiya a Nijeriya,” inji shi.

Idris ya kuma bayyana shirye-shiryen gwamnatin Tinubu na haɗa kai da NUJ wajen fuskantar muhimman matsalolin aikin jarida da suka haɗa da walwalar ma’aikata, daidaiton jinsi, da sauya fasalin aiki zuwa tsarin zamani.

“Muna da niyyar aiki tare da ku da kuma tallafa maku wajen fuskantar waɗannan matsaloli yayin da kuke ƙoƙarin daidaita kan ku da sabon yanayin ƙarni na 21,” inji shi.

Yayin da ya bayyana cewa ɗaya daga cikin manyan ayyukan kafafen yaɗa labarai shi ne sa ido kan ayyukan gwamnati, Ministan ya buƙace su da su riƙa kallon gwamnati a matsayin abokiyar aiki wajen gina Nijeriya mai zaman lafiya da cigaba.

“Ko da yake kuna da rawar da kuke takawa wajen sa ido a kan gwamnati – kuma muna maraba da hakan – akwai buƙatar ku riƙa kallon mu a matsayin abokan aiki, kuma masu haɗa kai wajen samar da zaman lafiya, tsaro da cigaba da ƙasar nan ke nema ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu,” inji ministan.

Ya kuma taya NUJ murna kan cikar ta shekaru 70 da kafuwa tare da yaba wa ƙungiyar kan ƙaddamar da wani littafi da ke bayyana tarihin ta.

“Ina da yaƙinin cewa aikin jarida yana da buƙatar ko yaushe ya riƙa bayyana labaran sa da kan sa da kuma tsara yadda za a bayyana shi; domin ba wani zai yi mana hakan ba,” inji shi.

Idris ya kuma yaba da girmamawa ga Shugaban Taron, Cif Aremu Olusegun Osoba, da kuma Mamallakin jaridar Vanguard, Mista Sam Amuka-Pemu, bisa gagarumar gudunmawar da suka bayar a harkar jarida da hidima ga jama’a, yana mai cewa su ne abin koyi a wannan sana’ar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kafafen yaɗa labarai aikin jarida

এছাড়াও পড়ুন:

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba

Ya zuwa ranar 23 ga watan Satumba agogon Beijing, kasashe 152 cikin 193 na Majalisar Dinkin Duniya sun amince da Falasdinu a matsayin kasa. A cikin kasashe biyar masu kujerun dindindin a kwamitin sulhun MDD, Amurka ce kadai ba ta amince da kafuwar kasar Falasdinu ba. Wannan guguwar ta amincewa da kafuwar kasar Falasdinu ta sanya Amurka da Isra’ila sun zama saniyar ware a fannin diflomasiyya game da batun rikicin Falasdinu da Isra’ila.

Wata kuri’ar jin ra’ayoyin jama’a da CGTN ta gudanar a duniya ta nuna cewa kashi 78.2 cikin 100 na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu sun yi imanin cewa, babbar hanyar warware matsalar Falasdinu ita ce aiwatar da shawarar “kafa kasashe biyu”, wadda kuma ita ce ginshikin samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya. Kashi 81.8 cikin 100 kuma sun bayyana cewa, “kafa kasa mai cin gashin kanta, mai cikakken ‘yanci ta Falasdinu bisa kan iyakokin da aka shata a shekarar 1967, tare da gabashin Kudus a matsayin babban birninta” ta zama wata matsaya da aka cimma a tsakanin kasashen duniya.

A cewar bayanai daga hukumomin kiwon lafiya na Gaza, hare-haren sojojin Isra’ila a Gaza sun yi sanadin mutuwar mutane 65,283 tare da jikkata wasu 166,575 tun bayan sabon rikicin da ya barke tsakanin Isra’ila da Falasdinu a ranar 7 ga watan Oktobar shekarar 2023. A kuri’ar jin ra’ayoyin, kashi 90.8 cikin 100 na wadanda suka yi Allah-wadai da ta’asar da Isra’ila ke tafkawa, kuma sun yi imanin cewa, ya kamata Isra’ila ta gaggauta dakatar da hare-harenta na soji a zirin Gaza. Kazalika, kashi 92.1 cikin 100 sun yi kira ga kasashen duniya da su dauki mataki tare da yin taron dangi wajen taka birki ga farmakin sojojin Isra’ila a Gaza. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
  • Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025?
  • Ballon d’Or: ’Yan wasa 5 da ke iya lashe kyautar 2025 
  • Babu Gwamnatin Sojin Da Ta Kai Ta  Tinubu Muni A Tarihin Nijeriya
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila