Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
Published: 17th, April 2025 GMT
Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta cika hannu da wani matashi da aka gani a wani yanayi mai kamanceceniya da baɗala da wata Akuya, lamarin da ya janyo cece-kuce a dandalin sada zumunta.
Matashin, Shamsu Yakubu mai shekaru 24 da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa ta Kano, ya shiga hannu ne bayan ɓullar wani bidiyonsa a dandalan sada zumunta musamman TikTok yana tsotsar farjin wata Akuya.
A cikin bidiyon da wani yake ɗaukarsa wanda ya yaɗu sosai a soshiyal midiya, an hasko matashin a wannan yanayin mai kama da baɗala tare da Akuyar.
Sai dai yayin da yake amsa tambayoyin mahukunta, matashin ya yi iƙirarin aikata hakan da nufin neman suna domin samun ɗaukaka ta dandalin sada zumunta.
Wannan lamari da ya fusata mazauna yankin ya sanya suka yi yunƙurin ɗaukar mataki a hannunsu, amma aka yi sa’a wani jami’in Hisbah ya tari hanzarinsu kuma aka cafke shi.
A yayin shan titsiye, matashin ya musanta zargin da ake yi masa, yana rantsuwa da Allah cewa bai tsotsi Akuyar ba.
“Na rantse da Allah ban tsotsi Akuyar ba, bakina kawai na kai kusa da wurin,” a cewarsa.
Matashin ya kuma bayyana cewa wannan shi ne karon farko da ya aikata irin wannan lamari yana mai nadamar cewa ba zai ƙara ba.
Sai dai duk da ya musanta cewa ba ya ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ko kayan maye, Hukumar Hisbah ta umarci a yi masa gwajin ƙwaƙwalwa.
Da yake martani kan lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah, Sheikh Aminuddeen Abubakar, ya yi Allah wadai yana mai cewa wannan abun kunya ya saɓa wa tarbiyya da koyarwar addinin Islama
“Abun takaici ne mutum ɗan Musulmi ya faɗa wannan abun kunya domin neman suna,” in ji Sheikh Aminuddeen.
Haka kuma, ya ce za a kai Akuyar Asibitin Dabbobi domin duba lafiyarta.
Sheikh Aminuddeen ya gargaɗi masu ƙoƙarin neman suna da wallafe-wallafen hofi marasa kan gado.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Akuya Baɗala Jihar Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35 Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
Na’urorin kakkabo jiragen sama na Iran sun kakkabo jirgin sama na HKI samfurin F-35 a yammacin kasar, wanda shi ne karo na uku a cikin sa’oi 24.
Kamfanin dillancin labarun Tasnim ya nakalto majiyar tsaro na cewa; dakarun kare samaniyar jamhuriyar musulunci sun harbo jirgin sama samfurin F-35,kuma matukinsa ya fito ta hanyar amfani da lemar ceto.
Bayan wani lokaci daga faduwar jrigin da kuma fitowar matukinsa daga ciki, sojojin kasa na jamhuriyar musulunci ta Iran sun kama shi.
A jiya Juma’a ma dai daakrun kare sararin samaniyar jamhuriyar musulunci ta Iran, sun kakkabo jiragen saman na ‘yan sahayoniya wadanda kirar Amurka ne, kuma daya daga cikin jiragen yakin da take alfahari da su.
Shi dai jirgin yakin na Amurka samfurin F-35 yana da layar zana, kuma da wuya na’urar hangen nesa-Radar- ta iya tsinkayo shi. Kudin kowane daya daga cikin wadannan jiragen shi ne dalar Amurka miliyan 100.