Aminiya:
2025-06-15@00:44:03 GMT

Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano

Published: 17th, April 2025 GMT

Hukumar Hisbah a Jihar Kano ta cika hannu da wani matashi da aka gani a wani yanayi mai kamanceceniya da baɗala da wata Akuya, lamarin da ya janyo cece-kuce a dandalin sada zumunta.

Matashin, Shamsu Yakubu mai shekaru 24 da ke zaune a Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa ta Kano, ya shiga hannu ne bayan ɓullar wani bidiyonsa a dandalan sada zumunta musamman TikTok yana tsotsar farjin wata Akuya.

Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas An naɗa mace ta farko mai magana da yawun rundunar sojin Nijeriya

A cikin bidiyon da wani yake ɗaukarsa wanda ya yaɗu sosai a soshiyal midiya, an hasko matashin a wannan yanayin mai kama da baɗala tare da Akuyar.

Sai dai yayin da yake amsa tambayoyin mahukunta, matashin ya yi iƙirarin aikata hakan da nufin neman suna domin samun ɗaukaka ta dandalin sada zumunta.

Wannan lamari da ya fusata mazauna yankin ya sanya suka yi yunƙurin ɗaukar mataki a hannunsu, amma aka yi sa’a wani jami’in Hisbah ya tari hanzarinsu kuma aka cafke shi.

A yayin shan titsiye, matashin ya musanta zargin da ake yi masa, yana rantsuwa da Allah cewa bai tsotsi Akuyar ba.

“Na rantse da Allah ban tsotsi Akuyar ba, bakina kawai na kai kusa da wurin,” a cewarsa.

Matashin ya kuma bayyana cewa wannan shi ne karon farko da ya aikata irin wannan lamari yana mai nadamar cewa ba zai ƙara ba.

Sai dai duk da ya musanta cewa ba ya ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ko kayan maye, Hukumar Hisbah ta umarci a yi masa gwajin ƙwaƙwalwa.

Da yake martani kan lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah, Sheikh Aminuddeen Abubakar, ya yi Allah wadai yana mai cewa wannan abun kunya ya saɓa wa tarbiyya da koyarwar addinin Islama

“Abun takaici ne mutum ɗan Musulmi ya faɗa wannan abun kunya domin neman suna,” in ji Sheikh Aminuddeen.

Haka kuma, ya ce za a kai Akuyar Asibitin Dabbobi domin duba lafiyarta.

Sheikh Aminuddeen ya gargaɗi masu ƙoƙarin neman suna da wallafe-wallafen hofi marasa kan gado.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Akuya Baɗala Jihar Kano

এছাড়াও পড়ুন:

  Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa

Na’urorin kakkabo jiragen sama na Iran sun kakkabo jirgin sama na HKI samfurin F-35  a yammacin kasar, wanda shi ne karo na uku a cikin sa’oi 24.

Kamfanin dillancin labarun Tasnim ya nakalto majiyar tsaro na cewa; dakarun kare samaniyar jamhuriyar musulunci sun harbo jirgin sama samfurin F-35,kuma matukinsa ya fito ta hanyar amfani da lemar ceto.

 Bayan wani lokaci daga faduwar jrigin da kuma fitowar matukinsa daga ciki, sojojin kasa na jamhuriyar musulunci ta Iran sun kama shi.

A jiya Juma’a ma dai daakrun kare sararin samaniyar jamhuriyar musulunci ta Iran, sun kakkabo jiragen saman na ‘yan sahayoniya wadanda kirar Amurka ne, kuma daya daga cikin jiragen yakin da take alfahari da su.

Shi dai jirgin yakin na Amurka samfurin F-35 yana da layar zana, kuma da wuya na’urar hangen nesa-Radar- ta iya tsinkayo shi. Kudin kowane daya daga cikin wadannan jiragen shi ne dalar Amurka miliyan 100.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita