HausaTv:
2025-09-19@02:41:36 GMT

Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium

Published: 16th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa babu batun tattaunawa kan shirin kasar na tace sinadarin Uranium wanda ke a matsayin wani bangare na shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.

Abbas Araghchi ya kuma ce tattaunawar Tehran da Washington ba za ta haifar da wani sakamako ba idan ana amfani da matsin mata lamba da rashin mutunta juna.

Mista Araghchi ya bayyana hakan ne a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin Iran na mako-mako a birnin Tehran babban birnin kasar, bayan da manzon musamman na Amurka Steve Witkoff ya ce Tehran “dole ne ta kawar da” shirinta na inganta makamashin nukiliya domin cimma matsaya da Washington.

Kalaman na zuwa ne a daidai lokacin da bangarorin ke shirin ganawa  a ranar Asabar.

Da ya tabo yunkurin da Amurka ke yi na matsin lamba kan Iran a yayin shawarwarin, ministan harkokin wajen na Iran ya ce: Matsayinmu da ayyukanmu a bayyane suke, ba za su cimma komai ta hanyar matsin lamba ba, idan aka yi shawarwarin a cikin yanayi na mutuntawa, za a iya samun ci gaba, amma babu abin da za a samu ta hanyar matsin lamba ba.

Araghchi ya kuma soki “wasu batutuwa masu cin karo da juna” da ke fitowa daga gwamnatin Trump gabanin tattaunawar ta ranar Asabar.

Dama tun farko Jagoran juyin juya halin musulinci na Iran, Ayatullah Khamenei ya bayyana a ranar Talata cewa tattaunawar Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani ta yi kyau a matakin farko, sai dai ya kara da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da matukar shakku ga daya bangaren.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista

Sabuwar mutum-mutumi ta fasahar AI da aka kirkira kuma aka nada mukamin minista a ƙasar Albania ta yi jawabi a karon farko a gaban majalisar dokokin kasar.

A ranar Alhamis ce dai ministan ya bayyana gaban majalisar, inda ya kare rawar da zai taka a gwamnati, yana mai cewa, “Ban zo don na maye gurbin mutane ba, sai dai don taimaka musu.”

Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja Gwamnatin Tarayya ta raba wa talakawa N330bn — Ministan Kuɗi

Wannan minista ta AI wacce aka sanya masa suna Diella, ma’ana “rana” a harshen Albania, ita ce ministar gwamnati ta farko a duniya da aka ƙirƙira ta hanyar fasahar AI.

Firaministan Albania, Edi Rama, ne ya naɗa shi a makon da ya gabata.

A cikin wani faifan bidiyo da aka nuna a majalisa, Diella ta bayyana a matsayin mace sanye da kayan gargajiya na Albania, inda ta ce: “Wasu sun ce ba na kan dokar kundin tsarin mulki saboda ni ba mutum ba ce.”

Diella ta ƙara da cewa: “Bari in tunatar da ku, babban hatsarin da ke tattare da kundin tsarin mulki ba na injuna ba ne, na masu mulki ne.”

A makon da ya gabata, Firaminista Rama ya bayyana cewa Diella za ta kula da dukkan al’amuran kwangiloli na gwamnati, domin tabbatar da cewa an kawar da cin hanci gaba ɗaya, kuma duk kuɗaɗen gwamnati da aka sanya a cikin tsarin kwangila za su kasance a bayyane.

An ƙaddamar da Diella a watan Janairu a matsayin mataimakiyar fasahar AI da ke taimaka wa jama’a wajen amfani da dandalin e-Albania, wanda ke bayar da takardu da ayyuka na gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
  • An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
  • Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista
  • Shugaban Kasar Iran Ya bayyana Yadda Hadin Gwiwa Tsakanin Iran Da Rasha Ya Kawo Ci Gaba Tsakaninsu
  • Rahoto: An gudanar da tattaunawa mai tsawo tsakanin Syria da Isra’ila a Landan
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai