Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
Published: 16th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa babu batun tattaunawa kan shirin kasar na tace sinadarin Uranium wanda ke a matsayin wani bangare na shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.
Abbas Araghchi ya kuma ce tattaunawar Tehran da Washington ba za ta haifar da wani sakamako ba idan ana amfani da matsin mata lamba da rashin mutunta juna.
Mista Araghchi ya bayyana hakan ne a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin Iran na mako-mako a birnin Tehran babban birnin kasar, bayan da manzon musamman na Amurka Steve Witkoff ya ce Tehran “dole ne ta kawar da” shirinta na inganta makamashin nukiliya domin cimma matsaya da Washington.
Kalaman na zuwa ne a daidai lokacin da bangarorin ke shirin ganawa a ranar Asabar.
Da ya tabo yunkurin da Amurka ke yi na matsin lamba kan Iran a yayin shawarwarin, ministan harkokin wajen na Iran ya ce: Matsayinmu da ayyukanmu a bayyane suke, ba za su cimma komai ta hanyar matsin lamba ba, idan aka yi shawarwarin a cikin yanayi na mutuntawa, za a iya samun ci gaba, amma babu abin da za a samu ta hanyar matsin lamba ba.
Araghchi ya kuma soki “wasu batutuwa masu cin karo da juna” da ke fitowa daga gwamnatin Trump gabanin tattaunawar ta ranar Asabar.
Dama tun farko Jagoran juyin juya halin musulinci na Iran, Ayatullah Khamenei ya bayyana a ranar Talata cewa tattaunawar Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani ta yi kyau a matakin farko, sai dai ya kara da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da matukar shakku ga daya bangaren.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin
Manyan jami’ai daga kasashe da dama da ke halartar taron tattaunawa na Tehran sun yi kira da a tattauna domin tunkarar manyan al’amura a yankin.
Manyan jami’ai daga kasashe 53 da suka hada da ministoci da masana da ne ke halartar taron na kwanaki biyu.
Ministan harkokin wajen Oman Badr bin Hamad Al Busaidi ya ce a halin yanzu yankin yammacin Asiya na fuskantar kalubale da dama da ke bukatar tattaunawa cikin gaggawa.
A yayin jawabin nasa, Ministan harkokin wajen Oman ya bayyana matukar damuwarsa kan tashe-tashen hankula da kisan kiyashin da al’ummar Falasdinu ke fuskanta, yana mai bayyana wannan lamari a matsayin wani abin takaici a duniya.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Tajikistan ya jaddada bukatar yin tattaunawa mai ma’ana don tinkarar manyan matsalolin da duniya ke fuskanta.
Armeniya ta bakin sakatarenta na komitin sulhu Armen Grigoryan ta tabbatar da aniyar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Shi kuwa tsohon firaministan kasar Iraki Adel Abdul-Mahdi ya bayyana matukar damuwarsa game da matsalar jin kai da kuma ci gaba da kisan kiyashi a zirin Gaza.
Ya yi Allah wadai da gazawar kasashen Larabawa da kungiyoyin kasa da kasa, wadanda a cewarsa, sun kasa dakile irin ta’asar da Isra’ila ke yi.