Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
Published: 16th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa babu batun tattaunawa kan shirin kasar na tace sinadarin Uranium wanda ke a matsayin wani bangare na shirin nukiliyar kasar na zaman lafiya.
Abbas Araghchi ya kuma ce tattaunawar Tehran da Washington ba za ta haifar da wani sakamako ba idan ana amfani da matsin mata lamba da rashin mutunta juna.
Mista Araghchi ya bayyana hakan ne a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin Iran na mako-mako a birnin Tehran babban birnin kasar, bayan da manzon musamman na Amurka Steve Witkoff ya ce Tehran “dole ne ta kawar da” shirinta na inganta makamashin nukiliya domin cimma matsaya da Washington.
Kalaman na zuwa ne a daidai lokacin da bangarorin ke shirin ganawa a ranar Asabar.
Da ya tabo yunkurin da Amurka ke yi na matsin lamba kan Iran a yayin shawarwarin, ministan harkokin wajen na Iran ya ce: Matsayinmu da ayyukanmu a bayyane suke, ba za su cimma komai ta hanyar matsin lamba ba, idan aka yi shawarwarin a cikin yanayi na mutuntawa, za a iya samun ci gaba, amma babu abin da za a samu ta hanyar matsin lamba ba.
Araghchi ya kuma soki “wasu batutuwa masu cin karo da juna” da ke fitowa daga gwamnatin Trump gabanin tattaunawar ta ranar Asabar.
Dama tun farko Jagoran juyin juya halin musulinci na Iran, Ayatullah Khamenei ya bayyana a ranar Talata cewa tattaunawar Iran da Amurka a birnin Muscat na kasar Omani ta yi kyau a matakin farko, sai dai ya kara da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da matukar shakku ga daya bangaren.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Bata Taba yin Watsi Da Diplomasiya Ba Amurka Ce Ke Kai Mutane Bango
Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi ya fadi cewa iran tana ci gaba da aiki da diplomasiya duk da cikas da Amurka take kawo wa a tattaunawar da ba ta kai tsaye ba, ganin cewa Amurka tana amfani da karfi wajen gudanar da harkokin duniya .
Yace idan bangaren Amurka ta nuna shirinta na yin tattaunawa bisa mutunta jina da kare munufofin kowa, to iran za ta iya duba lamarin, saboda bamu taba barin teburin tattaunawa ba , saboda it ace ingantacciyar hanya ta fuskantar alumma.
Dangane da Ziyarar da ya kai a bayan bayan nan a garin muscat da kuma tarurrukan da yayi, babban jami’in diplomasiyar iran yace babban abin takaici shi ne inda dokokin kasa da kasa da tsarin duniya suke kara yin tasiri ga yanayin Amurka na amfani da karfi a dangantakar kasa da kasa.
Daga karshe yace akwai bukatar gina tsaro a iyakokin kasashen yankin ba tare da tsoma bakin kasashen waje ma’abota girman kai ba, wanda wannan ne zai kara samar da yarda da zai sa akulla yarjejeniyar tsaro a yankin tekun fasha.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kungiyar ECOWAS Ya Gana Da Shugaban Mulki Soji Na Kasar Guinea Bissau December 2, 2025 An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran December 2, 2025 Araghchi: Halayyar Amurka ce yin matsin lamba maimakon diflomasiyya a dangantaka ta kasa da kasa December 2, 2025 Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Don Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi December 2, 2025 Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma December 2, 2025 Chuck Schumer: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela December 2, 2025 Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba December 2, 2025 Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci