HausaTv:
2025-12-08@15:40:37 GMT

‘Yan tawayen Sudan sun kafa tasu gwamnati

Published: 16th, April 2025 GMT

Yan tawaye a kasar Sudan sun sanar da kafa tasu gwamnati, bayan shekara biyu ana gwabza fada a kasar.

Shugaban rundinar kai daukin gaggawa ta (RSF), Mohamed Hamdan “Hemedti”, ya ce an kafa gwamnati a yankunan da kungiyarsa ke iko da su, musamman a yammacin Darfur.

Dagalo ya bayyana haka ne a wani jawabi da ya yi a ranar Talata, inda ya ce, “A wannan ranar tunawa, muna alfahari da ayyana kafa gwamnatin zaman lafiya da hadin kai.

 Ya kuma ce za a kafa majalisar shugaban kasa mai mambobi 15 da ke wakiltar dukkan yankunan Sudan.

Janar din wanda tuni Amurka ta kakabawa takunkumi bisa zarginsa da hannu a kisan kiyashin da aka yi a yankin Darfur, ya ce wasu kungiyoyi masu dauke da makamai kamar wani bangare na kungiyar ‘yantar da ‘yancin kai ta Sudan, sun shiga wannan gwamnatin.

Masana da daman a ganin wannan a matsayin koma baya ga duk wani yunkuri da ake na samar da zaman lafiya a wannan kasa.

Tun daga watan Afrilun 2023, ne fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na FSR ya barke lamarin da ya jefa kasar cikin rudani.

Akalla mutane 24,000 ne aka kashe, sannan Sama da mutane miliyan 13 ne suka rasa matsugunansu, ciki har da miliyan 4 da suka yi gudun hijira zuwa kasashe makwabta.

 A kwanakin baya ne dai shugaban mulkin sojin na Sudan, Janar Al-Burhan, ya sanar da kwace iko da Khartoum babban birnin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda

Bayan da ƙasashen biyu maƙwabtan juna na Congo da Rwanda suka sanya hannu a yarjejeniyar zaman lafiya da Donald Trump ya bayyana a matsayin mai cike da tarihi, jagoron na Amurka ya jinjinawa shugabannin ƙasashen biyu waɗanda ya ce sun yi hangen nesa wajen amincewa da kawo ƙarshen zubar da jinin dubban mutane tsawon shekaru.

An dai haska wannan zaman sanya hannu kai tsaye ta gidajen talabijin, inda shugabannin biyu wato Felix Tshisekedi na Jamhuriyyar Congo da Paul Kagame na Rwanda suka rattaɓa hannu a yarjejeniyar a gaban idon Donald Trump can a birnin Washington.

A cewar Trump shugabannin biyu sun ajje banbance-bambancen da ke tsakaninsu wajen rungumar zaman lafiya don jama’arsu.

Sai dai an sanya hannu a yarjejeniyar can a Washington dai dai lokacin da ake ganin ci gaban yaƙi tsakanin Sojin Congo da mayaƙan M23 da Rwanda ke marawa baya a kudancin lardin Kivu.

Babu dai wakilcin M23 a wannan tattaunawa ta Washington, hasalima basu aminta da yarjejeniyar da ka cimma a zaman ba, maimakon haka suna halartar nasu taron na daban wanda Qatar ke jagorantar sulhunta su da Congo a birnin Doha.

Masu sharhi na ganin  abu ne mai matuƙar wahala, yarjejeniyar ta birnin Washington ta yi tasiri wajen kawo ƙarshen wannan yaƙi na shekaru.

Yarjejeniyar na zuwa a dai dai lokacin da Amurka ke son zuba jari a ɓangaren haƙar ma’adinai a Congo inda a gefe guda itama Qatar ke faɗaɗa shirinta na zuba jari a ƙasashen Afrika.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
  • Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
  • Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi
  •  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada
  • Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan
  • Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika
  • Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026
  • Yaƙin M23 Ya ci Gaba a Congo Duk da Sulhu da Rwanda
  • Dorinar Ruwa ta Yi Ajalin Mutane Biyu, ta Raunata Shida a Gombe