HausaTv:
2025-11-13@08:57:09 GMT

‘Yan tawayen Sudan sun kafa tasu gwamnati

Published: 16th, April 2025 GMT

Yan tawaye a kasar Sudan sun sanar da kafa tasu gwamnati, bayan shekara biyu ana gwabza fada a kasar.

Shugaban rundinar kai daukin gaggawa ta (RSF), Mohamed Hamdan “Hemedti”, ya ce an kafa gwamnati a yankunan da kungiyarsa ke iko da su, musamman a yammacin Darfur.

Dagalo ya bayyana haka ne a wani jawabi da ya yi a ranar Talata, inda ya ce, “A wannan ranar tunawa, muna alfahari da ayyana kafa gwamnatin zaman lafiya da hadin kai.

 Ya kuma ce za a kafa majalisar shugaban kasa mai mambobi 15 da ke wakiltar dukkan yankunan Sudan.

Janar din wanda tuni Amurka ta kakabawa takunkumi bisa zarginsa da hannu a kisan kiyashin da aka yi a yankin Darfur, ya ce wasu kungiyoyi masu dauke da makamai kamar wani bangare na kungiyar ‘yantar da ‘yancin kai ta Sudan, sun shiga wannan gwamnatin.

Masana da daman a ganin wannan a matsayin koma baya ga duk wani yunkuri da ake na samar da zaman lafiya a wannan kasa.

Tun daga watan Afrilun 2023, ne fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na FSR ya barke lamarin da ya jefa kasar cikin rudani.

Akalla mutane 24,000 ne aka kashe, sannan Sama da mutane miliyan 13 ne suka rasa matsugunansu, ciki har da miliyan 4 da suka yi gudun hijira zuwa kasashe makwabta.

 A kwanakin baya ne dai shugaban mulkin sojin na Sudan, Janar Al-Burhan, ya sanar da kwace iko da Khartoum babban birnin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A Najeriya, an saba ganin jami’an ‘yan sanda suna gadin manyan mutane ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ko shugabanni maimakon su kasance a cikin al’umma suna tabbatar da tsaro ga kowa. Wannan tsarin ya haifar da tambayoyi masu zurfi game da adalci da yadda ake rarraba jami’an tsaro a ƙasar.

A halin da ake ciki, yawancin unguwanni da kauyuka na fama da ƙarancin jami’an ‘yan sanda, yayin da mutum guda ko wasu ‘yan kaɗan ke da ɗaruruwan masu tsaro a gefensu.
Ko yaya tasirin tura ‘yan sanda tsaron wasu daidaikun mutane maimakon tsaron alummar kasa gaba daya?

NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Ƙungiyar ASUU DAGA LARABA: Yadda ‘Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar Makamai

Wannan shine batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu
  • Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin
  • DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma
  • Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina
  • Sudan ta soki shirun kasashen duniya game ta’asar dake faruwa a kasar
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU
  • Sarkin Musulmi ya ba wa makarantu tallafin N1.3bn a Kebbi
  • Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5
  •  Kamaru: Jagoran ‘yan Hamayya Chiroma Ya Bai Wa Gwamnati Sa’o’i 48 Da Ta Saki Dukkanin Wadanda Aka Kama Bayan Tsabe
  • Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno