‘Yan tawayen Sudan sun kafa tasu gwamnati
Published: 16th, April 2025 GMT
Yan tawaye a kasar Sudan sun sanar da kafa tasu gwamnati, bayan shekara biyu ana gwabza fada a kasar.
Shugaban rundinar kai daukin gaggawa ta (RSF), Mohamed Hamdan “Hemedti”, ya ce an kafa gwamnati a yankunan da kungiyarsa ke iko da su, musamman a yammacin Darfur.
Dagalo ya bayyana haka ne a wani jawabi da ya yi a ranar Talata, inda ya ce, “A wannan ranar tunawa, muna alfahari da ayyana kafa gwamnatin zaman lafiya da hadin kai.
Ya kuma ce za a kafa majalisar shugaban kasa mai mambobi 15 da ke wakiltar dukkan yankunan Sudan.
Janar din wanda tuni Amurka ta kakabawa takunkumi bisa zarginsa da hannu a kisan kiyashin da aka yi a yankin Darfur, ya ce wasu kungiyoyi masu dauke da makamai kamar wani bangare na kungiyar ‘yantar da ‘yancin kai ta Sudan, sun shiga wannan gwamnatin.
Masana da daman a ganin wannan a matsayin koma baya ga duk wani yunkuri da ake na samar da zaman lafiya a wannan kasa.
Tun daga watan Afrilun 2023, ne fada tsakanin sojoji da dakarun kai daukin gaggawa na FSR ya barke lamarin da ya jefa kasar cikin rudani.
Akalla mutane 24,000 ne aka kashe, sannan Sama da mutane miliyan 13 ne suka rasa matsugunansu, ciki har da miliyan 4 da suka yi gudun hijira zuwa kasashe makwabta.
A kwanakin baya ne dai shugaban mulkin sojin na Sudan, Janar Al-Burhan, ya sanar da kwace iko da Khartoum babban birnin kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
Kungiyar ‘yan tawayen kasar DRC ta M23 ta kwace iko da wani gari mai muhimmanci bayan rushewar batun zaman lafiya
A jiya Juma’a ne dai kasar Amurka ta zargi kasar Rwanda da cewa ta keta yarjejeniyar sulhu da zaman lafita da ta kulla da DRC, tare da cewa, abinda Kigalin take yi shi ne jefa yankin zuwa yaki.
Mako daya da ya gabata ne dai aka kulla yarjejeniyar sulhu a tsakanin kasashen biyu wacce shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa; Ta tarihi ce.” Tare da nuna fatan ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin wanda ya dade cikin fadace-fadace.
Sai dai a ranar Larabar da ta gabata da yamma mayakan kungiyar M23 wacce Rwanda take goyawa baya sun sanar da kama garin Uvira wanda daya daga cikin muhimman wuraren da suke a hannun sojojin gwamnatin kasar a gabashin kasar.
Dama dai tun a baya wasu kwararru na MDD sun zargi Kigali da cewa, ita ce mai iko da akan dukkanin hare-haren da ‘yan tawayen suke kai wa a gabashin DRC.
Jakadan Amurka a MDD Mike Waltz ya ce; Amurka ba ta ji dadin abinda ya faru ba ko kadan, domin ya rusa yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla.
Su dai ‘yan tawayen ba su cikin yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla da Amurka kai tsaye, amma da suna cikin tattaunawar da ake yi da kasar Qatar.
Amurka dai ta shiga cikin Shirin zaman lafiya a cikin DRC, domin ta sami damar dibar ma’adanai da Allah ya huwacewa wannan kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara December 13, 2025 Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi December 13, 2025 Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci