Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar
Published: 16th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar ya jogoranci wata ziyarar aiki zuwa makobciyuar kasar Jamhuriyar Nijar.
Wannan it ace ziyara irinta ta farko da ministan harkokin wajen Najeriya ya kai a Jamhuriyar Nijar tun bayan da sojoji karkashin jagorancin Janar Abdourahmane Tiani suka kifar da mulkin farar hula na Mohamed Bazoum a watan Yulin shekarar 2023.
Juyin mulkin da sojojin sukayi a Nijar ya haifar da takaddamar diflomasiyya sosai tsakanin Nijar da kuma kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke jagoranta a wannan karon.
Batun mayar da hambararen shugaban Nijar Bazoum da kin lamuncewa juyin mulkin daga gwamnatin Najeriya da kuma kungiyar ta ECOWAS, shi ne a sahun gaba a takaddamar.
ECOWAS ta kakabawa Nijar tsauraren takunkumai tare kuma da yi mata barazanar daukan matakin soji idan sojojin basu mayar da Bazoum ba kan madafun iko.
Da alama dai wannan ziyarar ta ministan harkokin wajen Najeriyar zai yayafawa takun-sakar dake tsakanin kasashen makobtan juna masu raba iyaka da al’adu iri daya musamman a yankin arewacin Najeriya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Tehran ya bukaci tattaunawa cikin gaggawa kan kalubalen yankin
Manyan jami’ai daga kasashe da dama da ke halartar taron tattaunawa na Tehran sun yi kira da a tattauna domin tunkarar manyan al’amura a yankin.
Manyan jami’ai daga kasashe 53 da suka hada da ministoci da masana da ne ke halartar taron na kwanaki biyu.
Ministan harkokin wajen Oman Badr bin Hamad Al Busaidi ya ce a halin yanzu yankin yammacin Asiya na fuskantar kalubale da dama da ke bukatar tattaunawa cikin gaggawa.
A yayin jawabin nasa, Ministan harkokin wajen Oman ya bayyana matukar damuwarsa kan tashe-tashen hankula da kisan kiyashin da al’ummar Falasdinu ke fuskanta, yana mai bayyana wannan lamari a matsayin wani abin takaici a duniya.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Tajikistan ya jaddada bukatar yin tattaunawa mai ma’ana don tinkarar manyan matsalolin da duniya ke fuskanta.
Armeniya ta bakin sakatarenta na komitin sulhu Armen Grigoryan ta tabbatar da aniyar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Shi kuwa tsohon firaministan kasar Iraki Adel Abdul-Mahdi ya bayyana matukar damuwarsa game da matsalar jin kai da kuma ci gaba da kisan kiyashi a zirin Gaza.
Ya yi Allah wadai da gazawar kasashen Larabawa da kungiyoyin kasa da kasa, wadanda a cewarsa, sun kasa dakile irin ta’asar da Isra’ila ke yi.