Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar
Published: 16th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar ya jogoranci wata ziyarar aiki zuwa makobciyuar kasar Jamhuriyar Nijar.
Wannan it ace ziyara irinta ta farko da ministan harkokin wajen Najeriya ya kai a Jamhuriyar Nijar tun bayan da sojoji karkashin jagorancin Janar Abdourahmane Tiani suka kifar da mulkin farar hula na Mohamed Bazoum a watan Yulin shekarar 2023.
Juyin mulkin da sojojin sukayi a Nijar ya haifar da takaddamar diflomasiyya sosai tsakanin Nijar da kuma kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke jagoranta a wannan karon.
Batun mayar da hambararen shugaban Nijar Bazoum da kin lamuncewa juyin mulkin daga gwamnatin Najeriya da kuma kungiyar ta ECOWAS, shi ne a sahun gaba a takaddamar.
ECOWAS ta kakabawa Nijar tsauraren takunkumai tare kuma da yi mata barazanar daukan matakin soji idan sojojin basu mayar da Bazoum ba kan madafun iko.
Da alama dai wannan ziyarar ta ministan harkokin wajen Najeriyar zai yayafawa takun-sakar dake tsakanin kasashen makobtan juna masu raba iyaka da al’adu iri daya musamman a yankin arewacin Najeriya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi.
Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan dake baiyana cewa rashin aikin yi ya karu a najeriya da kaso 5.3 a farkon wannan shekarar, kazalika binciken ya baiyana cewa wadanda basu yi karatu mai zurfi ba sun fi wadanda suka yi karatu mai zurfi samun aikin yi.
NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon LafiyaWadansu dalilai ne ke kara kawo rashin aikin yi a Najeriya?
Wadansu hanyoyi za’a bi wajen magance rashin aikin yi?
Wadannan da ma wasu tambayoyi na cikin batutuwan da Shirin Najeriya A Yau zai yi duba akai.
Domin sauke shirin, latsa nan