HausaTv:
2025-07-05@18:33:43 GMT

Ministan harkokin wajen Najeriya Ya kai ziyara Nijar

Published: 16th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar ya jogoranci wata ziyarar aiki zuwa makobciyuar kasar Jamhuriyar Nijar.

Wannan it ace ziyara irinta ta farko da ministan harkokin wajen Najeriya ya kai a Jamhuriyar Nijar tun bayan da sojoji karkashin jagorancin Janar Abdourahmane Tiani suka kifar da mulkin farar hula na Mohamed Bazoum a watan Yulin shekarar 2023.

Juyin mulkin da sojojin sukayi a Nijar ya haifar da takaddamar diflomasiyya sosai tsakanin Nijar da kuma kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ke jagoranta a wannan karon.

Batun mayar da hambararen shugaban Nijar Bazoum da kin lamuncewa juyin mulkin daga gwamnatin Najeriya da kuma kungiyar ta ECOWAS, shi ne a sahun gaba a takaddamar.

ECOWAS ta kakabawa Nijar tsauraren takunkumai tare kuma da yi mata barazanar daukan matakin soji idan sojojin basu mayar da Bazoum ba kan madafun iko.

Da alama dai wannan ziyarar ta ministan harkokin wajen Najeriyar zai yayafawa takun-sakar dake tsakanin kasashen makobtan juna masu raba iyaka da al’adu iri daya musamman a yankin arewacin Najeriya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

A yau Asabar ne ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da takwaran aikinsa na kasar Ghana Samuel Okudzeto Ablakwa, suka aikewa juna sakon murnar cika shekaru 65, da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen biyu.

A cikin sakonsa Wang Yi ya bayyana cewa, cikin shekaru 65, an raya dangantaka tsakanin Sin da Ghana yadda ya kamata, kana an karfafa imani da juna kan harkokin siyasa, tare da samun manyan nasarori a hadin gwiwarsu ta fannoni daban daban. Kazalika, sassan biyu sun goyi bayan juna a fannin kulawa da harkokin kasa da kasa.

Wang Yi ya ce, ana fatan yin kokari tare da minista Ablakwa, wajen kara fadada mu’ammala a tsakanin ma’aikatun harkokin wajen kasashen biyu, da goyon bayan juna, da aiwatar da manufofi da aka amince da su, a gun taron koli na Beijing, na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, don sa kaimi ga daga dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da Ghana zuwa sabon matsayi.

A nasa bangare, minista Ablakwa ya bayyana cewa, kasar Ghana na godewa Sin, bisa samar mata da gudummawa, da goyon baya a fannonin raya tattalin arziki da zamantakewar al’umma. Ya ce an samu manyan nasarori a fannin hadin gwiwar sassan biyu karkashin tsarin dandalin FOCAC, wanda hakan ya samar da babbar gudummawa ga kasashen Afirka ciki har da Ghana, wajen inganta karfinsu na samun ci gaba, kuma hakan zai amfani jama’ar kasashen Afirka baki daya. Bugu da kari, kasar Ghana tana fatan kokartawa tare da kasar Sin, wajen sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare yadda ya kamata. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta?
  • Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  •  Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC