Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta kammala shirye-shirye domin fara taron bita ga maniyyata aikin Hajjin bana.

Shugaban Hukumar, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir  ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Ilori.

Ya shawarci dukkan maniyyata da su halarci wannan muhimmin shiri, yana mai  cewa za a tattauna muhimman batutuwa da suka shafi yadda ake gudanar da ibadar Hajji.

Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa za a fara gudanar da taron bitar ne a harabar Hukumar Jin Daɗin Alhazai  ta Jihar  daga ranar Lahadi, 20 ga watan Afirilun 2025.

Shugaban ya ƙara da cewa babban limamin masallacin Juma’a na Ilori, Sheikh Imam Mohammed Bashir, tare da wasu malaman addini daga sassa daban-daban na jihar za su jagoranci addu’a ta musamman domin samun tsaro da nasara ga maniyyatan.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Malami ya ƙara da cewa suna da cikakken shiri da azama don fuskantar APC da kuma kawo canji mai ma’ana a Nijeriya.

“Mun yanke shawarar fuskantar gwamnati mai ci domin yaƙi da matsalolin tsaro da yunwa, tare da mayar da Nijeriya kan hanyar da ta dace,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jihar Jigawa Ta Bukaci Karamar Hukumar Roni Ta Samar Da Karin Ajujuwa Ga Fulani Makiyaya
  • Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu
  • Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano
  •  A Yau Juma’a Ne Ake Gudanar Da Taron Karrama Shahid Birgediya Janar Husain Salami A Nan Birnin Tehran
  • An Gudanar Da Taron Girmama Shahidan Yakin Kwanaki 12 A Nan Tehran
  • Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara