Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
Published: 16th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta kammala shirye-shirye domin fara taron bita ga maniyyata aikin Hajjin bana.
Shugaban Hukumar, Alhaji Abdulsalam Abdulkadir ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Ilori.
Ya shawarci dukkan maniyyata da su halarci wannan muhimmin shiri, yana mai cewa za a tattauna muhimman batutuwa da suka shafi yadda ake gudanar da ibadar Hajji.
Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa za a fara gudanar da taron bitar ne a harabar Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar daga ranar Lahadi, 20 ga watan Afirilun 2025.
Shugaban ya ƙara da cewa babban limamin masallacin Juma’a na Ilori, Sheikh Imam Mohammed Bashir, tare da wasu malaman addini daga sassa daban-daban na jihar za su jagoranci addu’a ta musamman domin samun tsaro da nasara ga maniyyatan.
Ali Muhammad Rabi’u
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jihar Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Malami ya ƙara da cewa suna da cikakken shiri da azama don fuskantar APC da kuma kawo canji mai ma’ana a Nijeriya.
“Mun yanke shawarar fuskantar gwamnati mai ci domin yaƙi da matsalolin tsaro da yunwa, tare da mayar da Nijeriya kan hanyar da ta dace,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp