Aminiya:
2025-09-17@23:19:40 GMT

Budurwar da ke rayuwa a banɗaki don gudun biyan kuɗin hayar gida

Published: 15th, April 2025 GMT

Wata budurwa ’yar kasar China ta janyo muhawara a shafukan sada zumunta bayan ta nuna masaukinta da ba a saba gani ba — banɗaki mai faɗin ƙafa 6 a wurin aikinta, wanda ta biya kuɗin China Yuan 50 kacal, kwatankwacin Naira dubu 10 da dari 533.

Kowa yana ƙoƙari ya tara kudi, amma mutum nawa ne za su yarda su kwana a banɗaki don tara kuɗi?

HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS

Wannan budurwa ’yar garin Hunan a ƙasar China, ta girgiza duniya kwanan nan, bayan ta wallafa hotunan wajen zamanta da ba a saba gani ba – wani ƙaramin banɗaki da ba a amfani da shi a cikin masana’antar kayan cikin gidaje da take aiki.

Matar mai shekara 19 ta bayyana cewa, ta fito daga dangi matalauta kuma ba za ta iya biyan sama da Yuan 800 kwatankwacin Naira dubu dari 168 da 537 don biyan kuɗin ɗakin da ya dace, don haka ta tambayi maigidanta ko za ta iya zama a banɗakin.

Wallafa rubutun nata ya yi tasiri, inda yawancin mutanen da suka yi tsokaci sun ce tana yaɗa hotuna da bidiyo ne kawai don jan hankali saboda babu wanda zai iya rayuwa a cikin irin wannan yanayi.

Sai dai maigidan matar ya yi amfani da kafar sada zumunta intanet, inda ya tabbatar da cewa, lallai tana kwana a banɗaki mai kafa 6 a masana’antarsa.

“Ta dage kan da ta ta biya ƙarin kuɗi Yuan 50 — kwatankwacin Naira dubu 10 da dari 533 na ruwa da wutar lantarki a kowane wata gwara ta kwana bandaki, amma ba na son daukar kudinta,” in ji shugaban matar.

Matar ta ce, maigidan nata ya yi kokarin taimaka mata ta nemo gidan haya kusa da masana’antar, amma kuɗin haya ya kai kimanin Yuan 800 ($ 110) zuwa Yuan 1,000 kwatankwacin Naira dubu dari 210 da dari 6 da 72.

A halin yanzu tana karɓar albashin ƙasa da Yuan 3,000 — kwatankwacin Naira dubu dari 6 da dubu 32 da 17, kuma tana ƙoƙarin yin tanadin kuɗi mai yawa don biyan kudin hayar gida, don haka take ganin hakan bai dace.

Har ma ya ba ta damar zama a ofis a masana’antar, amma ta yanke shawarar cewa za ta fi samun sirri a banɗakin da ba a amfani da shi.

“A wajena yanzu na samu wurin zama,” budurwar ta wallwafa a intanet cewa, “ba na so in kashe kuɗi da yawa wajen yin hayar gida. Tabbas ba zan iya jure kashe Yuan 800 don hayar gida ba.”

Bayan da sakon ya yaɗu, matar ta bayyana cewa, ta daina karatu tun tana shekara 16 domin ta taimaka wa danginta da kuɗi, wanda hakan ya sa wannan aikin ya fi mata muhimmanci.

Kimanin wata guda ke nan tana zaune a cikin ƙaramin banɗakin.

Yanayin rayuwar budurwar ya samu ra’ayoyi mabambanta a shafukan sada zumunta na kasar China, inda wasu suka yaba da ƙudurinta na yin tanadin kuɗi, wasu kuma na cewa, lafiyarta ta fi kuɗi muhimmanci, kuma babu wanda ya isa ya rayu cikin wannan yanayi sai dai idan ba shi da wata mafita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Banɗaki budurwa kwatankwacin Naira dubu

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar