Aminiya:
2025-11-13@20:20:57 GMT

Budurwar da ke rayuwa a banɗaki don gudun biyan kuɗin hayar gida

Published: 15th, April 2025 GMT

Wata budurwa ’yar kasar China ta janyo muhawara a shafukan sada zumunta bayan ta nuna masaukinta da ba a saba gani ba — banɗaki mai faɗin ƙafa 6 a wurin aikinta, wanda ta biya kuɗin China Yuan 50 kacal, kwatankwacin Naira dubu 10 da dari 533.

Kowa yana ƙoƙari ya tara kudi, amma mutum nawa ne za su yarda su kwana a banɗaki don tara kuɗi?

HOTUNA: Zulum ya karɓi baƙuncin Majalisar Sarakunan Arewa a Borno Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS

Wannan budurwa ’yar garin Hunan a ƙasar China, ta girgiza duniya kwanan nan, bayan ta wallafa hotunan wajen zamanta da ba a saba gani ba – wani ƙaramin banɗaki da ba a amfani da shi a cikin masana’antar kayan cikin gidaje da take aiki.

Matar mai shekara 19 ta bayyana cewa, ta fito daga dangi matalauta kuma ba za ta iya biyan sama da Yuan 800 kwatankwacin Naira dubu dari 168 da 537 don biyan kuɗin ɗakin da ya dace, don haka ta tambayi maigidanta ko za ta iya zama a banɗakin.

Wallafa rubutun nata ya yi tasiri, inda yawancin mutanen da suka yi tsokaci sun ce tana yaɗa hotuna da bidiyo ne kawai don jan hankali saboda babu wanda zai iya rayuwa a cikin irin wannan yanayi.

Sai dai maigidan matar ya yi amfani da kafar sada zumunta intanet, inda ya tabbatar da cewa, lallai tana kwana a banɗaki mai kafa 6 a masana’antarsa.

“Ta dage kan da ta ta biya ƙarin kuɗi Yuan 50 — kwatankwacin Naira dubu 10 da dari 533 na ruwa da wutar lantarki a kowane wata gwara ta kwana bandaki, amma ba na son daukar kudinta,” in ji shugaban matar.

Matar ta ce, maigidan nata ya yi kokarin taimaka mata ta nemo gidan haya kusa da masana’antar, amma kuɗin haya ya kai kimanin Yuan 800 ($ 110) zuwa Yuan 1,000 kwatankwacin Naira dubu dari 210 da dari 6 da 72.

A halin yanzu tana karɓar albashin ƙasa da Yuan 3,000 — kwatankwacin Naira dubu dari 6 da dubu 32 da 17, kuma tana ƙoƙarin yin tanadin kuɗi mai yawa don biyan kudin hayar gida, don haka take ganin hakan bai dace.

Har ma ya ba ta damar zama a ofis a masana’antar, amma ta yanke shawarar cewa za ta fi samun sirri a banɗakin da ba a amfani da shi.

“A wajena yanzu na samu wurin zama,” budurwar ta wallwafa a intanet cewa, “ba na so in kashe kuɗi da yawa wajen yin hayar gida. Tabbas ba zan iya jure kashe Yuan 800 don hayar gida ba.”

Bayan da sakon ya yaɗu, matar ta bayyana cewa, ta daina karatu tun tana shekara 16 domin ta taimaka wa danginta da kuɗi, wanda hakan ya sa wannan aikin ya fi mata muhimmanci.

Kimanin wata guda ke nan tana zaune a cikin ƙaramin banɗakin.

Yanayin rayuwar budurwar ya samu ra’ayoyi mabambanta a shafukan sada zumunta na kasar China, inda wasu suka yaba da ƙudurinta na yin tanadin kuɗi, wasu kuma na cewa, lafiyarta ta fi kuɗi muhimmanci, kuma babu wanda ya isa ya rayu cikin wannan yanayi sai dai idan ba shi da wata mafita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Banɗaki budurwa kwatankwacin Naira dubu

এছাড়াও পড়ুন:

An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba

Shugabannin jam’iyyar APC a matakin unguwanni 35 da sakatarorinsu a faɗin Jihar Kuros Riba, sun nemi a tsige shugaban jam’iyyar na jihar, Mista Alphonsus Eba, bisa zargin badaƙala da kuɗaɗen jam’iyya da kuma nuna son kai wajen gudanar da harkokin jam’iyyar.

Wannan buƙatar ta fito ne a cikin wata sanarwa da shugabanni da sakatarorin jam’iyyar suka rattaba wa hannu bayan taron da suka gudanar a garin Kalaba, babban birnin jihar, a ranar Talata.

Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda a Borno

Shugabannin sun bayyana cewa idan ba a ɗauki mataki kan shugaban ba, akwai yiwuwar rikicin cikin gida ya durƙushe jam’iyyar a jihar.

Da yake jawabi bayan taron, shugaban ƙungiyar shugabannin, Cif Kelvin Njong, ya shaida wa Aminiya cewa sun gamsu cewa shugaban jam’iyyar na jihar yana amfani da dukiyar jam’iyya yadda yake so ba tare da tuntubar kowa ba.

“Muna zargin shugaban jam’iyyar da wadaƙa da kuɗaɗen jam’iyya. Ba ya bin tsarin jam’iyya kuma ba ya jin shawarar kowa. Wannan ne dalilin da ya sa muke son a sauke shi domin a samu shugabanci nagari,” in ji shi.

Sun kuma zargi shugaban jam’iyyar da nuna bambanci da son kai ga wasu ’ya’yan jam’iyyar, lamarin da suka ce ya saɓa wa wasu sassa na kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC da aka sabunta a watan Maris na 2022.

Haka kuma, shugabannin sun yi zargin cewa Alphonsus Eba ya ƙi raba kuɗaɗen da aka samu daga sayar da fom ga ‘yan takara a zaɓen 2023 yadda ya kamata, musamman ga shugabannin jam’iyyar a ƙananan hukumomi da mazabu.

“Akwai shugabanni da sakatarori har mutum 5,778 a matakai daban-daban, amma an ce naira miliyan 9.2 kawai aka raba daga cikin miliyoyin da aka tara.

“Shugabannin jiha su kaɗai ne aka bai wa naira miliyan 40. Wannan rashin adalci ne kuma ya saba da tsarin jam’iyya,” in ji su.

Sun kuma buƙaci a gudanar da cikakken bincike kan yadda shugaban ya riƙa kashe kuɗaɗen jam’iyya da sunan ayyuka, tare da buƙatar a tabbatar da raba kaso 70 cikin 100 na kuɗaɗen jam’iyya ga ƙananan hukumomi, mazabu, da gundumomi.

Ɗaya daga cikin shugabannin jam’iyyar a ƙaramar hukumar Bekwarra, Kwamared Odama Thomas Odama, ya ce: “Abin da muke cewa gaskiya ne, ba bita-da-ƙulli muke yi masa ba. Shugaban ya ci amana kuma hakan ya jawo ɓacin ran ’ya’yan jam’iyyar.”

Shi ma sakataren ƙungiyar shugabannin jam’iyyar APC a matakin ƙananan hukumomi, William Book, ya jaddada cewa duk zarge-zargen da aka ambata gaskiya ne.

“Ba zargin na shaci faɗi muke yi masa ba, akwai hujjoji da takardu da ke tabbatar da abin da muke faɗi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane
  • Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Majalisa ta amince da buƙatar Tinubu na karɓo rancen N1.15bn
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • An Bayyana Ranar Karshe Ta Biyan Kudin Aikin Hajji Mai Zuwa
  • Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu
  • An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori