Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5
Published: 5th, July 2025 GMT
A wani rahoton musamman da jaridar ” Telegraph” ta Birtaniya ta buga, ta amabci cewa; makamai masu linzami da Iran ta harba wa Isra’ila sun sauka kai tsaye akan wasu muhimman cibiyoyin soja.
Jaridar ta kara da cewa; Mahukuntan Isra’ila ba su bayyana wa duniya wadannan wuraren da makamai masu linzamin su ka fadawa ba, saboda aiki da dokar soja ta Sakaye labaran wuraren da aka kai wa hare-hare.
Rahoton jaridar ya ce, ya sami bayanai ne daga hotunan tauraron dan’adam na jamiar Jahar Oregon da suka saba yin aiki da irin wadannan bayana da suke tarawa domin gano barnar da aka yi a wuraren yaki.
Rahoton ya ci gaba da cewa cibiyoyin sojan da Iran ta kai wa harin, a baya ba a yi Magana akansu ba, sai yanzu kuma suna a cikin yankunan arewa, kudanci da tsakiyar ne. Daga cikin wuraren da akwai sansanin sojan sama mafi girma, cibiyar tattara bayanai na sirri, da kuma wata cibiya ta ajiyar kayan yaki.
A jiya juma’a sojojin HKI sun ki amsa tambayar jaridar ta Telegraph akan zurfin asarar da hare-haren na Iran su ka yi wa cibiyoyin nasu.
Sai dai kuma jaridar ta ce, wadannan sabbin cibiyoyin sojan da ake Magana makamai masu linzami na Iran sun suka a cikinsu,kari ne akan wasu 36 da Iran din kai wa farmaki, wadanda na’urorin da HKI take takama da su na kakkabo makamai, su ka kasa tare su, kuma sun yi barna mai girman gaske.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
Rahotanni daga kudanci Lebanon sun ce, sau uku jiragen yakin HKI su ka kai hare-hare a kan gidajen mutane da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya da kuma jikkatar wasu da dama.
A garin Shaqra’dake yankin Bint-jubail, jiragen sama marasa matuki sun kai hare-hare da ya yi sanadiyyar jikkatar mutane biyu da raunuka, kamar yadda ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar.
Har ila yau wani jirgin maras matuki na abokan gaba ya kai wani harin akan wata mota a yankin “Safful-Hawa” da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya.
A garin Shab’a kuwa ‘yan sahayoniyar sun kai hari akan wani gida, wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutanen dake cikinsa.
Majiyar asibiti a garin Marja’iyyun ta ce an kai mata wani mutum wanda ya sami raunuka masu hatsari.
HKI dai tana ci gaba da kai hare-hare akan kasar Lebanon bayan tsagaita wutar yaki a shekarar da ta gabata.