A wani rahoton musamman da jaridar ” Telegraph” ta Birtaniya ta buga,  ta amabci cewa; makamai masu linzami da Iran ta harba wa Isra’ila sun sauka kai tsaye akan wasu muhimman cibiyoyin soja.

Jaridar ta kara da cewa; Mahukuntan Isra’ila ba su bayyana wa duniya wadannan wuraren da makamai masu linzamin su ka fadawa ba, saboda aiki da dokar soja ta Sakaye labaran wuraren da aka kai wa hare-hare.

Rahoton jaridar ya ce, ya sami bayanai ne daga hotunan tauraron dan’adam na jamiar Jahar Oregon da suka saba yin aiki da irin wadannan bayana da suke tarawa domin gano barnar da aka yi a wuraren yaki.

Rahoton ya ci gaba da cewa cibiyoyin sojan da Iran ta kai wa harin, a baya ba a yi Magana akansu ba, sai yanzu kuma suna a cikin yankunan arewa, kudanci da tsakiyar ne. Daga cikin  wuraren da akwai sansanin sojan sama mafi girma, cibiyar tattara bayanai na sirri, da kuma wata cibiya ta ajiyar kayan yaki.

A jiya juma’a sojojin HKI sun ki amsa tambayar jaridar ta Telegraph akan zurfin asarar da hare-haren na Iran su ka yi wa cibiyoyin nasu.

Sai dai kuma jaridar ta ce, wadannan sabbin cibiyoyin sojan da ake Magana makamai masu linzami na  Iran sun suka a cikinsu,kari ne akan wasu 36 da Iran din kai wa farmaki, wadanda na’urorin da HKI take takama da su na kakkabo makamai, su ka kasa tare su, kuma sun yi barna mai girman gaske.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A  HKI
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato