Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Published: 5th, July 2025 GMT
Salim Sani Shehu
Jam’iyyar NNPP ta bayyana a hukumance cewa tsohon ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ba zai sake yin takarar shugaban ƙasa karkashin jam’iyyar a zaɓen 2027 ba.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Agbo Major, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin da yake mayar da martani ga kalaman Buba Galadima, wanda ya ce Kwankwaso zai ci gaba da zama cikin jam’iyyar kuma zai tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027.
Major ya ce jam’iyyar ta riga ta kori Kwankwaso da Galadima bisa zargin aikata laifukan cin amanar jam’iyya, don haka ba su da ikon magana da sunan NNPP, balle su wakilci jam’iyyar a a duk wani sha’anin siyasa.
“Tun da dadewa NNPP ta sallami Kwankwaso da Galadima, don haka ba su da hurumin magana da sunan jam’iyya ko amfani da ita a wajen neman wata kujera ta siyasa,” in ji shi.
Major ya jaddada cewa babu maganar bai wa Kwankwaso tikitin takarar shugaban ƙasa kai-tsaye kamar yadda aka ba shi a zaɓen 2023, wannan karon hakan ba zai maimaitu ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kwankwaso takara Zaɓe Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa
A ranar nuna goyon baya ga alummar falasdinu shugaban kasar Pakistan Asif Ali zardari ya jinjinawa Alummar falasdinu game da juriya da tsayin Dakar da suka nuna, yace jarumtar da suka nuna ta bude sabon shafin tarihi, don haka gudanar da bincike kan laifukan yaki da HKI ta tafka yana da muhimmanci sosai.
Kasar Pakistan tana da tarihin nuna goyon bayan alummar falasdinu , inda suka nuna goyon bayan alummar falasdinu na hakkin fayyacewa kansu makoma, a kudurin Lahore na shekara ta 1940,don haka wannan kiran na zardari ya kara jaddada tsohon matsayin Pakistan da ya doru kan nuna goyon baya, kwatar yanci da daidaito da kuma adalci.
Kiran da zardari yayi na gudanar da bincike kan laifukan yakin Israila yana nuna irin yadda kasashen musulmi suka damu da rashin daukar matakin doka kan ayyukan da isra’ila ke yi .
Ana sa ran Pakistan za ta ci gaba da fafutukar ganin an baiwa falasdinawa goyon baya a mataki na kasa da kasa, tana bukatar ganin an dakatar da bude wuta ta dindindin yadda za’a isar da kayan agaji, da kuma amincewa da falasdinu a matsayin kasa, kuma Pakistan za ta ci gaba da karfafa sakonninta na diplomasiya tare da bayyana ayyukan isra’ila a matsayin wadanda suka keta doka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro November 29, 2025 Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12 November 29, 2025 Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya November 29, 2025 Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya November 29, 2025 MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa November 29, 2025 Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci